< Job 19 >

1 respondens autem Iob dixit
Sai Ayuba ya amsa,
2 usquequo adfligitis animam meam et adteritis me sermonibus
“Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
3 en decies confunditis me et non erubescitis opprimentes me
Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
4 nempe et si ignoravi mecum erit ignorantia mea
In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
5 at vos contra me erigimini et arguitis me obprobriis meis
In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
6 saltim nunc intellegite quia Deus non aequo iudicio adflixerit me et flagellis suis me cinxerit
sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
7 ecce clamabo vim patiens et nemo audiet vociferabor et non est qui iudicet
“Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
8 semitam meam circumsepsit et transire non possum et in calle meo tenebras posuit
Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
9 spoliavit me gloria mea et abstulit coronam de capite meo
Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
10 destruxit me undique et pereo et quasi evulsae arbori abstulit spem meam
Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
11 iratus est contra me furor eius et sic me habuit quasi hostem suum
Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
12 simul venerunt latrones eius et fecerunt sibi viam per me et obsederunt in gyro tabernaculum meum
Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
13 fratres meos longe fecit a me et noti mei quasi alieni recesserunt a me
“Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
14 dereliquerunt me propinqui mei et qui me noverant obliti sunt mei
Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
15 inquilini domus meae et ancillae meae sicut alienum habuerunt me et quasi peregrinus fui in oculis eorum
Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
16 servum meum vocavi et non respondit ore proprio deprecabar illum
Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
17 halitum meum exhorruit uxor mea et orabam filios uteri mei
Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
18 stulti quoque despiciebant me et cum ab eis recessissem detrahebant mihi
Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
19 abominati sunt me quondam consiliarii mei et quem maxime diligebam aversatus est me
Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
20 pelli meae consumptis carnibus adhesit os meum et derelicta sunt tantummodo labia circa dentes meos
Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
21 miseremini mei miseremini mei saltim vos amici mei quia manus Domini tetigit me
“Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
22 quare persequimini me sicut Deus et carnibus meis saturamini
Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
23 quis mihi tribuat ut scribantur sermones mei quis mihi det ut exarentur in libro
“Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
24 stilo ferreo et plumbi lammina vel certe sculpantur in silice
a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
25 scio enim quod redemptor meus vivat et in novissimo de terra surrecturus sim
Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
26 et rursum circumdabor pelle mea et in carne mea videbo Deum
Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
27 quem visurus sum ego ipse et oculi mei conspecturi sunt et non alius reposita est haec spes mea in sinu meo
Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
28 quare ergo nunc dicitis persequamur eum et radicem verbi inveniamus contra eum
“In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
29 fugite ergo a facie gladii quoniam ultor iniquitatum gladius est et scitote esse iudicium
sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”

< Job 19 >