< Job 14 >

1 homo natus de muliere brevi vivens tempore repletus multis miseriis
“Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
2 quasi flos egreditur et conteritur et fugit velut umbra et numquam in eodem statu permanet
Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
3 et dignum ducis super huiuscemodi aperire oculos tuos et adducere eum tecum in iudicium
Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
4 quis potest facere mundum de inmundo conceptum semine nonne tu qui solus es
Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
5 breves dies hominis sunt numerus mensuum eius apud te est constituisti terminos eius qui praeterire non poterunt
An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
6 recede paululum ab eo ut quiescat donec optata veniat sicut mercennarii dies eius
Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
7 lignum habet spem si praecisum fuerit rursum virescit et rami eius pullulant
“Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
8 si senuerit in terra radix eius et in pulvere emortuus fuerit truncus illius
Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
9 ad odorem aquae germinabit et faciet comam quasi cum primum plantatum est
Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
10 homo vero cum mortuus fuerit et nudatus atque consumptus ubi quaeso est
Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
11 quomodo si recedant aquae de mari et fluvius vacuefactus arescat
Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
12 sic homo cum dormierit non resurget donec adteratur caelum non evigilabit nec consurget de somno suo
haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
13 quis mihi hoc tribuat ut in inferno protegas me ut abscondas me donec pertranseat furor tuus et constituas mihi tempus in quo recorderis mei (Sheol h7585)
“Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol h7585)
14 putasne mortuus homo rursum vivet cunctis diebus quibus nunc milito expecto donec veniat inmutatio mea
In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
15 vocabis et ego respondebo tibi operi manuum tuarum porriges dexteram
Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
16 tu quidem gressus meos dinumerasti sed parces peccatis meis
Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
17 signasti quasi in sacculo delicta mea sed curasti iniquitatem meam
Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
18 mons cadens defluet et saxum transfertur de loco suo
“Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
19 lapides excavant aquae et adluvione paulatim terra consumitur et homines ergo similiter perdes
yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
20 roborasti eum paululum ut in perpetuum pertransiret inmutabis faciem eius et emittes eum
Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
21 sive nobiles fuerint filii eius sive ignobiles non intelleget
Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
22 attamen caro eius dum vivet dolebit et anima illius super semet ipso lugebit
Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”

< Job 14 >