< Psalmorum 94 >

1 Psalmus David, Quarta sabbati. Deus ultionum Dominus: Deus ultionum libere egit.
Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
2 Exaltare qui iudicas terram: redde retributionem superbis.
Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
3 Usquequo peccatores Domine: usquequo peccatores gloriabuntur:
Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
4 Effabuntur, et loquentur iniquitatem: loquentur omnes, qui operantur iniustitiam?
Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
5 Populum tuum Domine humiliaverunt: et hereditatem tuam vexaverunt.
Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
6 Viduam, et advenam interfecerunt: et pupillos occiderunt.
Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
7 Et dixerunt: Non videbit Dominus, nec intelliget Deus Iacob.
Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
8 Intelligite insipientes in populo: et stulti aliquando sapite.
Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
9 Qui plantavit aurem, non audiet? aut qui finxit oculum, non considerat?
Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
10 Qui corripit gentes, non arguet: qui docet hominem scientiam?
Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
11 Dominus scit cogitationes hominum, quoniam vanae sunt.
Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
12 Beatus homo, quem tu erudieris Domine: et de lege tua docueris eum.
Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
13 Ut mitiges ei a diebus malis: donec fodiatur peccatori fovea.
kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
14 Quia non repellet Dominus plebem suam: et hereditatem suam non derelinquet.
Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
15 Quoadusque iustitia convertatur in iudicium: et qui iuxta illam omnes qui recto sunt corde.
Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
16 Quis consurget mihi adversus malignantes? aut quis stabit mecum adversus operantes iniquitatem?
Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
17 Nisi quia Dominus adiuvit me: paulominus habitasset in inferno anima mea. (questioned)
Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
18 Si dicebam: Motus est pes meus: misericordia tua Domine adiuvabat me.
Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
19 Secundum multitudinem dolorum meorum in corde meo: consolationes tuae laetificaverunt animam meam.
Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
20 Numquid adhaeret tibi sedes iniquitatis: qui fingis laborem in praecepto?
Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
21 Captabunt in animam iusti: et sanguinem innocentem condemnabunt.
Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
22 Et factus est mihi Dominus in refugium: et Deus meus in adiutorium spei meae.
Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
23 Et reddet illis iniquitatem ipsorum: et in malitia eorum disperdet eos: disperdet illos Dominus Deus noster.
Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.

< Psalmorum 94 >