< Psalmorum 69 >
1 Psalmus David, in finem, pro iis, qui commutabuntur. Salvum me fac Deus: quoniam intraverunt aquae usque ad animam meam.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
2 Infixus sum in limo profundi: et non est substantia. Veni in altitudinem maris: et tempestas demersit me.
Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
3 Laboravi clamans, raucae factae sunt fauces meae: defecerunt oculi mei, dum spero in Deum meum.
Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
4 Multiplicati sunt super capillos capitis mei, qui oderunt me gratis. Confortati sunt qui persecuti sunt me inimici mei iniuste: quae non rapui, tunc exolvebam.
Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
5 Deus tu scis insipientiam meam: et delicta mea a te non sunt abscondita.
Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
6 Non erubescant in me qui expectant te Domine, Domine virtutum. Non confundantur super me qui quaerunt te, Deus Israel.
Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
7 Quoniam propter te sustinui opprobrium: operuit confusio faciem meam.
Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
8 Extraneus factus sum fratribus meis, et peregrinus filiis matris meae.
Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
9 Quoniam zelus domus tuae comedit me: et opprobria exprobrantium tibi, ceciderunt super me.
gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
10 Et operui in ieiunio animam meam: et factum est in opprobrium mihi.
Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
11 Et posui vestimentum meum cilicium: et factus sum illis in parabolam.
sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
12 Adversum me loquebantur qui sedebant in porta: et in me psallebant qui bibebant vinum.
Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
13 Ego vero orationem meam ad te Domine: tempus beneplaciti Deus. In multitudine misericordiae tuae exaudi me, in veritate salutis tuae:
Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
14 Eripe me de luto, ut non infigar: libera me ab iis, qui oderunt me, et de profundis aquarum.
Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
15 Non me demergat tempestas aquae, neque absorbeat me profundum: neque urgeat super me puteus os suum.
Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
16 Exaudi me Domine, quoniam benigna est misericordia tua: secundum multitudinem miserationum tuarum respice in me.
Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
17 Et ne avertas faciem tuam a puero tuo: quoniam tribulor, velociter exaudi me.
Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
18 Intende animae meae, et libera eam: propter inimicos meos eripe me.
Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
19 Tu scis improperium meum, et confusionem meam, et reverentiam meam.
Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
20 In conspectu tuo sunt omnes qui tribulant me, improperium expectavit cor meum et miseriam. Et sustinui qui simul contristaretur, et non fuit: et qui consolaretur, et non inveni.
Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
21 Et dederunt in escam meam fel: et in siti mea potaverunt me aceto.
Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
22 Fiat mensa eorum coram ipsis in laqueum, et in retributiones, et in scandalum.
Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
23 Obscurentur oculi eorum ne videant: et dorsum eorum semper incurva.
Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
24 Effunde super eos iram tuam: et furor irae tuae comprehendat eos.
Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
25 Fiat habitatio eorum deserta: et in tabernaculis eorum non sit qui inhabitet.
Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
26 Quoniam quem tu percussisti, persecuti sunt: et super dolorem vulnerum meorum addiderunt.
Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
27 Appone iniquitatem super iniquitatem eorum: et non intrent in iustitiam tuam.
Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
28 Deleantur de Libro viventium: et cum iustis non scribantur.
Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
29 Ego sum pauper et dolens: salus tua Deus suscepit me.
Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
30 Laudabo nomen Dei cum cantico: et magnificabo eum in laude:
Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
31 Et placebit Deo super vitulum novellum: cornua producentem et ungulas.
Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
32 Videant pauperes et laetentur: quaerite Deum, et vivet anima vestra:
Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
33 Quoniam exaudivit pauperes Dominus: et vinctos suos non despexit.
Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
34 Laudent illum caeli et terra, mare, et omnia reptilia in eis.
Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
35 Quoniam Deus salvam faciet Sion: et aedificabuntur civitates Iuda. Et inhabitabunt ibi, et hereditate acquirent eam.
gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
36 Et semen servorum eius possidebit eam, et qui diligunt nomen eius, habitabunt in ea.
’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.