< Psalmorum 68 >
1 Psalmus Cantici David, in finem. Exurgat Deus, et dissipentur inimici eius, et fugiant qui oderunt eum, a facie eius.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă tashi, bari a watsar da abokan gābansa; bari maƙiyansa su gudu a gabansa.
2 Sicut deficit fumus, deficiant: sicut fluit cera a facie ignis, sic pereant peccatores a facie Dei.
Kamar yadda iska take hura hayaƙi, bari yă hura su haka; kamar yadda kaki kan narke a gaban wuta, bari mugaye su hallaka a gaban Allah.
3 Et iusti epulentur, et exultent in conspectu Dei: et delectentur in laetitia.
Amma bari adalai su yi murna su kuma yi farin ciki a gaban Allah; bari su yi murna da farin ciki.
4 Cantate Deo, psalmum dicite nomini eius: iter facite ei, qui ascendit super occasum: Dominus nomen illi. Exultate in conspectu eius, turbabuntur a facie eius,
Rera wa Allah, rera yabo ga sunansa, ku ɗaukaka wanda yake hawa a kan gizagizai; sunansa Ubangiji ne, ku kuma yi farin ciki a gabansa.
5 patris orphanorum, et iudicis viduarum. Deus in loco sancto suo:
Uba ga marayu, mai kāre gwauraye, shi ne Allah a mazauninsa mai tsarki.
6 Deus qui inhabitare facit unius moris in domo: Qui educit vinctos in fortitudine, similiter eos, qui exasperant, qui habitant in sepulchris.
Allah ya shirya masu kaɗaici a cikin iyalai, ya jagorance’yan kurkuku da waƙoƙi; amma’yan tawaye suna zama a ƙasa mai zafin rana.
7 Deus cum egredereris in conspectu populi tui, cum pertransires in deserto:
Sa’ad da ka fito a gaban mutanenka, ya Allah, sa’ad da ka taka ta cikin ƙasar da take wofi, (Sela)
8 Terra mota est, etenim caeli distillaverunt a facie Dei Sinai, a facie Dei Israel.
duniya ta girgiza, sammai suka zuba ruwan sama, a gaban Allah, wanda ya bayyana a Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra’ila.
9 Pluviam voluntariam segregabis Deus hereditati tuae: et infirmata est, tu vero perfecisti eam.
Ka ba da yayyafi a yalwace, ya Allah; ka rayar da gādonka da ya gāji.
10 Animalia tua habitabunt in ea: parasti in dulcedine tua pauperi, Deus.
Mutanenka suka zauna a cikinsa, kuma daga yalwarka, ya Allah, ka tanada wa matalauta.
11 Dominus dabit verbum evangelizantibus, virtute multa.
Ubangiji ya yi umarni, mutane masu yawa ne suka yi shelarsa,
12 Rex virtutum dilecti dilecti: et speciei domus dividere spolia.
“Sarakuna da mayaƙa suka gudu a gaggauce; cikin sansani mutane sun raba ganima.
13 Si dormiatis inter medios cleros, pennae columbae deargentatae, et posteriora dorsi eius in pallore auri.
Har yayinda kuke barci a cikin garken tumaki, an dalaye fikafikan kurciya da azurfa, fikafikanta da zinariya mai ƙyalli.”
14 Dum discernit caelestis reges super eam, nive dealbabuntur in Selmon:
Sa’ad da Maɗaukaki ya watsar da sarakuna a cikin ƙasa, sai ya zama kamar ƙanƙara ta sauka a kan Zalmon.
15 mons Dei, mons pinguis. Mons coagulatus, mons pinguis:
Duwatsun Bashan, duwatsu masu alfarma ne; duwatsun Bashan masu wuyar hawa ne.
16 ut quid suspicamini montes coagulatos? Mons, in quo beneplacitum est Deo habitare in eo: etenim Dominus habitabit in finem.
Don me kuke duba da kishi, ya duwatsu masu wuyan hawa, a kan dutsen da Allah ya zaɓa yă yi mulki, inda Ubangiji kansa zai zauna har abada?
17 Currus Dei decem millibus multiplex, millia laetantium: Dominus in eis in Sina in sancto.
Karusan Allah ninkin dubbai goma ne da kuma dubu dubbai; Ubangiji ya zo daga Sinai ya shiga cikin haikalinsa.
18 Ascendisti in altum, cepisti captivitatem: accepisti dona in hominibus: Etenim non credentes, inhabitare Dominum Deum.
Sa’ad da ka hau bisa, ka bi da kamammu cikin tawagarka; ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga’yan tawaye, don kai, ya Ubangiji Allah, za ka zauna a can.
19 Benedictus Dominus die quotidie: prosperum iter faciet nobis Deus salutarium nostrorum.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, ga Allah Mai Cetonmu, wanda kullum yake ɗaukan nauyinmu. (Sela)
20 Deus noster, Deus salvos faciendi: et Domini Domini exitus mortis.
Allahnmu shi ne Allah wanda yake ceto; daga Ubangiji Mai Iko Duka kuɓuta yake zuwa daga mutuwa.
21 Verumtamen Deus confringet capita inimicorum suorum: verticem capilli perambulantium in delictis suis.
Tabbatacce Allah zai murƙushe kawunan abokan gābansa, rawanin gashi na waɗanda suke ci gaba cikin zunubansa.
22 Dixit Dominus: Ex Basan convertam, convertam in profundum maris:
Ubangiji ya ce, “Zan kawo su daga Bashan; zan kawo su daga zurfafan teku,
23 Ut intingatur pes tuus in sanguine: lingua canum tuorum ex inimicis, ab ipso.
don ku wanke ƙafafunku a cikin jinin maƙiyanku, yayinda harsunan karnukanku su sami rabonsu.”
24 Viderunt ingressus tuos Deus, ingressus Dei mei: regis mei qui est in sancto.
Jerin gwanonka ya zo a bayyane, ya Allah, jerin gwanon Allahna da Sarkina zuwa cikin wuri mai tsarki.
25 Praevenerunt principes coniuncti psallentibus, in medio iuvencularum tympanistriarum.
A gaba akwai mawaƙa, a bayansu akwai makaɗa; tare da su akwai’yan mata suna bugan ganguna.
26 In ecclesiis benedicite Deo Domino, de fontibus Israel.
Ku yabi Allah cikin taro mai girma; yabi Ubangiji cikin taron Isra’ila.
27 Ibi Beniamin adolescentulus, in mentis excessu. Principes Iuda, duces eorum: principes Zabulon, principes Nephthali.
Ga ƙaramar kabilar Benyamin, suna jagorance su, ga babbar ƙungiya shugabannin Yahuda, ga kuma shugabannin Zebulun da na Naftali.
28 Manda Deus virtuti tuae: confirma hoc Deus, quod operatus es in nobis.
Ka bayyana ikonka, ya Allah; ka nuna ƙarfinka, ya Allah, kamar yadda ka yi a dā.
29 A templo tuo in Ierusalem, tibi offerent reges munera.
Saboda haikalinka a Urushalima sarakuna za su kawo maka kyautai.
30 Increpa feras arundinis, congregatio taurorum in vaccis populorum: ut excludant eos, qui probati sunt argento. Dissipa gentes, quae bella volunt:
Ka tsawata wa naman jejin nan a cikin kyauro, garken bijimai a cikin’yan maruƙan al’ummai. Ka ƙasƙantar, bari yă kawo sandunan azurfa. Ka watsar da al’ummai waɗanda suke jin daɗin yaƙi.
31 venient legati ex Aegypto: Aethiopia praeveniet manus eius Deo.
Jakadu za su zo daga Masar; Kush za tă miƙa kanta ga Allah.
32 Regna terrae, cantate Deo: psallite Domino: psallite Deo.
Ku rera wa Allah, ya masarautan duniya, ku rera yabo ga Ubangiji, (Sela)
33 qui ascendit super caelum caeli, ad Orientem. Ecce dabit voci suae vocem virtutis,
gare shi wanda yake hawan daɗaɗɗen sararin sama, wanda yake tsawa da babbar murya.
34 date gloriam Deo super Israel, magnificentia eius, et virtus eius in nubibus.
Ku yi shelar ikon Allah, wanda ɗaukakarsa take a bisa Isra’ila, wanda ikonsa yake a cikin sarari.
35 Mirabilis Deus in sanctis suis, Deus Israel ipse dabit virtutem, et fortitudinem plebi suae, benedictus Deus.
Kai mai banmamaki ne, ya Allah, cikin wurinka mai tsarki; Allah na Isra’ila yakan ba da iko da kuma ƙarfi ga mutanensa. Yabo ya tabbata ga Allah!