< Psalmorum 60 >
1 Psalmus In finem, Pro his, qui immutabuntur, in tituli inscriptionem David in doctrinam, cum succendit Mesopotamiam Syriam, et Sobal, et convertit Ioab, et percussit Edom in valle Salinarum duodecim millia. Deus repulisti nos, et destruxisti nos: iratus es, et misertus es nobis.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin Alkawari.” Wani miktam ta Dawuda. Don koyarwa. Sa’ad da ya yaƙi Aram-Naharayim da Aram-Zoba, da kuma sa’ad da Yowab ya dawo ya bugi mutanen Edom dubu goma sha biyu a Kwarin Gishiri. Ka ki mu, ya Allah, ka kuma fashe kāriyarmu; ka yi fushi da mu, yanzu ka mai da mu!
2 Commovisti terram, et conturbasti eam: sana contritiones eius, quia commota est.
Ka girgiza ƙasar ka kuma tsaga ta; ka daure karayarta, gama tana rawa.
3 Ostendisti populo tuo dura: potasti nos vino compunctionis.
Ka nuna wa mutanenka lokutan wahala; ka ba mu ruwan inabin da ya sa muka bugu.
4 Dedisti metuentibus te significationem: ut fugiant a facie arcus: Ut liberentur dilecti tui:
Amma ga waɗanda suke tsoronka, ka ɗaga tuta don a buɗe gāba da baka. (Sela)
5 salvum fac dextera tua, et exaudi me.
Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
6 Deus locutus est in sancto suo: Laetabor, et partibor Sichimam: et convallem tabernaculorum metibor.
Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Da nasara zan rarraba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
7 Meus est Galaad, et meus est Manasses: et Ephraim fortitudo capitis mei. Iuda rex meus:
Gileyad nawa ne, Manasse kuma nawa ne; Efraim shi ne hular kwanona, Yahuda kuma sandar mulkina.
8 Moab olla spei meae. In Idumaeam extendam calceamentum meum: mihi alienigenae subditi sunt.
Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirarin nasara.”
9 Quis deducet me in civitatem munitam? quis deducet me usque in Idumaeam?
Wa zai kawo ni birnin katanga? Wa zai bishe ni zuwa Edom?
10 Nonne tu Deus, qui repulisti nos: et non egredieris Deus in virtutibus nostris?
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
11 Da nobis auxilium de tribulatione: quia vana salus hominis.
Ka ba mu gudummawa a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
12 In Deo faciemus virtutem: et ipse ad nihilum deducet tribulantes nos.
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattake abokan gābanmu.