< Psalmorum 3 >
1 Psalmus David, Cum fugeret a facie Absalom filii sui. Domine quid multiplicati sunt qui tribulant me? multi insurgunt adversum me.
Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
2 Multi dicunt animae meae: Non est salus ipsi in Deo eius.
Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
3 Tu autem Domine susceptor meus es, gloria mea, et exaltans caput meum.
Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
4 Voce mea ad Dominum clamavi: et exaudivit me de monte sancto suo.
Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
5 Ego dormivi, et soporatus sum: et exurrexi, quia Dominus suscepit me.
Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
6 Non timebo millia populi circumdantis me: exurge Domine: salvum me fac Deus meus.
Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
7 Quoniam tu percussisti omnes adversantes mihi sine causa: dentes peccatorum contrivisti.
Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
8 Domini est salus: et super populum tuum benedictio tua.
Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)