< Psalmorum 130 >

1 Canticum graduum. De profundis clamavi ad te Domine:
Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
2 Domine exaudi vocem meam: Fiant aures tuae intendentes, in vocem deprecationis meae.
Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
3 Si iniquitates observaveris Domine: Domine quis sustinebit?
In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
4 Quia apud te propitiatio est: et propter legem tuam sustinui te Domine. Sustinuit anima mea in verbo eius:
Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
5 speravit anima mea in Domino.
Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
6 A custodia matutina usque ad noctem: speret Israel in Domino.
Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
7 Quia apud Dominum misericordia: et copiosa apud eum redemptio.
Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
8 Et ipse redimet Israel, ex omnibus iniquitatibus eius.
Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.

< Psalmorum 130 >