< Psalmorum 122 >

1 Canticum graduum. Laetatus sum in his, quae dicta sunt mihi: In domum Domini ibimus.
Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
2 Stantes erant pedes nostri, in atriis tuis Ierusalem.
Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
3 Ierusalem, quae aedificatur ut civitas: cuius participatio eius in idipsum.
An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
4 Illuc enim ascenderunt tribus, tribus Domini: testimonium Israel ad confitendum nomini Domini.
A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
5 Quia illic sederunt sedes in iudicio, sedes super domum David.
A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
6 Rogate quae ad pacem sunt Ierusalem: et abundantia diligentibus te.
Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
7 Fiat pax in virtute tua: et abundantia in turribus tuis.
Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
8 Propter fratres meos, et proximos meos, loquebar pacem de te:
Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
9 Propter domum Domini Dei nostri, quaesivi bona tibi.
Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.

< Psalmorum 122 >