< Liber Numeri 34 >
1 Locutusque est Dominus ad Moysen, dicens:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Praecipe filiis Israel, et dices ad eos: Cum ingressi fueritis Terram Chanaan, et in possessionem vobis sorte ceciderit, his finibus terminabitur.
“Ka umarci Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga Kan’ana, ƙasar da aka ba ku gādo za tă kasance da waɗannan iyakoki.
3 Pars meridiana incipiet a solitudine Sin, quae est iuxta Edom: et habebit terminos contra Orientem mare salsissimum.
“‘Gefenku na kudu zai haɗa da wani sashin Hamadan Zin ta iyakar Edom. A gabas, iyakarku ta kudu za tă fara daga ƙarshen Tekun Gishiri,
4 qui circuibunt australem plagam per ascensum Scorpionis, ita ut transeant in Senna, et perveniant ad meridiem usque ad Cadesbarne, unde egredientur confinia ad villam nomine Adar, et tendent usque ad Asemona.
tă ƙetare Mashigin Kunama a kudu, tă ci gaba zuwa Zin, sa’an nan tă nufi kudu da Kadesh Barneya. Sa’an nan za tă zarce zuwa Hazar Addar, tă nausa zuwa Azmon,
5 ibitque per gyrum terminus ab Asemona usque ad Torrentem Aegypti, et maris magni littore finietur.
inda za tă juya tă haɗu da Rafin Masar, tă kuma ƙarasa a Bahar Rum.
6 Plaga autem occidentalis a mari magno incipiet, et ipso fine claudetur.
“‘Iyakarku a yammanci, za tă kasance bakin Bahar Rum. Wannan ce za tă zama iyakarku a yamma.
7 Porro ad septentrionalem plagam a mari magno termini incipient, pervenientes usque ad montem altissimum,
“‘Iyakarku a arewanci kuwa za tă tashi daga Bahar Rum zuwa Dutsen Hor,
8 a quo venient in Emath usque ad terminos Sedada:
za tă kuma tashi daga Dutsen Hor, zuwa Lebo Hamat. Sa’an nan tă miƙe zuwa Zedad,
9 ibuntque confinia usque ad Zephrona, et villam Enan. hi erunt termini in parte Aquilonis.
tă ci gaba zuwa Zifron, sa’an nan tă ƙarasa a Hazar-Enan. Wannan ce za tă zama iyakarku a arewa.
10 Inde metabuntur fines contra orientalem plagam de villa Enan usque Sephama,
“‘Iyakarku a gabashi, za tă tashi daga Hazar-Enan zuwa Shefam.
11 et de Sephama descendent termini in Reblatha contra fontem Daphnim: inde pervenient contra Orientem ad mare Cenereth,
Iyakar za tă gangara daga Shefam zuwa Ribla a gefen gabashin Ayin, sa’an nan tă ci gaba a gangaren gabashin Tekun Kinneret.
12 et tendent usque ad Iordanem, et ad ultimum salsissimo claudentur mari. Hanc habebitis Terram per fines suos in circuitu.
Sa’an nan tă gangara ta Urdun, tă ƙarasa a Tekun Gishiri. “‘Wannan za tă zama ƙasarku, tare da iyakokinta a kowane gefe.’”
13 Praecepitque Moyses filiis Israel, dicens: Haec erit Terra, quam possidebitis sorte, et quam iussit Dominus dari novem tribubus, et dimidiae tribui.
Sai Musa ya umarci Isra’ilawa ya ce, “Ku raba wannan ƙasa da za ku gāda ta hanyar jefa ƙuri’a. Ubangiji ya umarta cewa a ba da ita ga kabilu tara da rabi,
14 Tribus enim filiorum Ruben per familias suas, et tribus filiorum Gad iuxta cognationum numerum, media quoque tribus Manasse,
saboda iyalan kabilar Ruben, kabilar Gad da rabin kabilar Manasse sun riga sun sami gādonsu.
15 id est, duae semis tribus, acceperunt partem suam trans Iordanem contra Iericho ad orientalem plagam.
Waɗannan kabilu biyu da rabi, sun sami gādonsu a wancan hayin Urdun a gabashin Yeriko wajen fitowar rana.”
16 Et ait Dominus ad Moysen:
Ubangiji ya ce wa Musa,
17 Haec sunt nomina virorum, qui Terram vobis divident, Eleazar sacerdos, et Iosue filius Nun,
“Waɗannan su ne sunayen mutanen da za su raba muku ƙasar gādo. Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun.
18 et singuli principes de tribubus singulis,
Ka kuma naɗa shugaba guda ɗaya daga kowace kabila domin yă taimaka a rabon ƙasar.
19 quorum ista sunt vocabula: De tribu Iuda, Caleb filius Iephone.
“Ga sunayensu. “Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
20 De tribu Simeon, Samuel filius Ammiud.
Shemuyel ɗan Ammihud, daga kabilar Simeyon
21 De tribu Beniamin, Elidad filius Chaselon.
Elidad ɗan Kislon, daga kabilar Benyamin;
22 De tribu filiorum Dan, Bocci filius Iogli.
Bukki ɗan Yogli, shugaba daga kabilar Dan;
23 Filiorum Ioseph de tribu Manasse, Haniel filius Ephod.
Hanniyel ɗan Efod, shugaba daga kabilar Manasse ɗan Yusuf;
24 De tribu Ephraim, Camuel filius Sephthan.
Kemuwel ɗan Shiftan, shugaba daga kabilar Efraim ɗan Yusuf;
25 De tribu Zabulon, Elisaphan filius Pharnach.
Elizafan ɗan Farnak, shugaba daga kabilar Zebulun;
26 De tribu Issachar, dux Phaltiel filius Ozan.
Faltiyel ɗan Azzan, shugaba daga kabilar Issakar;
27 De tribu Aser, Ahiud filius Salomi.
Ahihud ɗan Shelomi, shugaba daga kabilar Asher;
28 De tribu Nephthali, Phedael filius Ammiud.
Fedahel ɗan Ammihud, shugaba daga kabilar Naftali.”
29 Hi sunt, quibus praeceperat Dominus ut dividerent filiis Israel Terram Chanaan.
Waɗannan su ne mutanen da Ubangiji ya umarta su raba gādo ga Isra’ilawa a ƙasar Kan’ana.