< Liber Numeri 31 >

1 Locutusque est Dominus ad Moysen, dicens:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Ulciscere prius filios Israel de Madianitis, et sic colligeris ad populum tuum.
“Ka ɗaukar wa Isra’ilawa fansa, a kan Midiyawa. Bayan wannan za ka mutu, a kuwa tara ka ga mutanenka.”
3 Statimque Moyses, Armate, inquit, ex vobis viros ad pugnam, qui possint ultionem Domini expetere de Madianitis.
Saboda haka Musa ya ce wa mutane, “Ku shirya waɗansu daga cikin mazanku, su tafi su yi yaƙi da Midiyawa don su ɗaukar wa Ubangiji fansa a kansu.”
4 mille viri de singulis tribubus eligantur ex Israel qui mittantur ad bellum.
Ku aiki maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
5 Dederuntque millenos de singulis tribubus, id est, duodecim millia expeditorum ad pugnam:
Saboda haka aka samo mayaƙa dubu goma sha biyu shiryayyu don yaƙi, maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
6 quos misit Moyses cum Phinees filio Eleazari sacerdotis, vasaque sancta, et tubas ad clangendum tradidit ei.
Musa ya aike su zuwa yaƙi, dubu ɗaya daga kowace kabila, tare da Finehas ɗan Eleyazar, firist, wanda ya ɗauki kayayyaki daga wuri mai tsarki da ƙahoni don kiran yaƙi.
7 Cumque pugnassent contra Madianitas atque vicissent, omnes mares occiderunt,
Suka yi yaƙi da Midiyawa, suka kashe kowane mutum yadda Ubangiji ya umarci Musa.
8 et reges eorum Evi, et Recem, et Sur, et Hur, et Rebe, quinque principes gentis: Balaam quoque filium Beor interfecerunt gladio.
A cikin waɗanda aka kashe kuwa akwai Ewi, Rekem, Zur, Hur da Reba; sarakuna biyar na Mediyawa. Suka kuma kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi.
9 Ceperuntque mulieres eorum, et parvulos, omniaque pecora, et cunctam supellectilem: quidquid habere potuerant depopulati sunt:
Isra’ilawa suka kwashe mata da yaran Midiyawa, a matsayin bayi. Suka kwashe shanunsu da tumakinsu da kuma dukan dukiyarsu, a matsayin ganima.
10 tam urbes quam viculos et castella flamma consumpsit.
Suka ƙone dukan garuruwan da Midiyawa suke zama, da dukan sansaninsu.
11 Et tulerunt praedam, et universa quae ceperant tam ex hominibus quam ex iumentis,
Suka kwashe dukan ganima haɗe da mutane da dabbobi,
12 et adduxerunt ad Moysen, et Eleazarum sacerdotem, et ad omnem multitudinem filiorum Israel. reliqua autem utensilia portaverunt ad castra in campestribus Moab iuxta Iordanem contra Iericho.
suka kawo bayi da ganiman nan, wurin Musa da Eleyazar firist, da kuma jama’ar Isra’ilawa, a sansaninsu a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko.
13 Egressi sunt autem Moyses, et Eleazar sacerdos, et omnes principes synagogae in occursum eorum extra castra.
Musa, da Eleyazar firist da dukan shugabannin jama’a, suka fito suka tarye su a bayan sansani.
14 Iratusque Moyses principibus exercitus, tribunis, et centurionibus qui venerant de bello,
Musa kuwa ya husata da shugabannin sojojin da suke shugabannin dubbai da shugabannin ɗari-ɗarin da suka dawo daga yaƙi.
15 ait: Cur feminas reservastis?
Ya tambaye su ya ce, “Kun bar dukan mata da rai?
16 Nonne istae sunt, quae deceperunt filios Israel ad suggestionem Balaam, et praevaricari vos fecerunt in Dominum super peccato Phogor, unde et percussus est populus?
Su ne waɗanda suka bi shawarar Bala’am suka kuma zama sanadin sa Isra’ilawa suka juya wa Ubangiji baya, har ya kawo abin da ya faru da Feyor, har annoba ya kashe dukan mutanen Ubangiji.
17 Ergo cunctos interficite quidquid est generis masculinis, etiam in parvulis: et mulieres, quae noverunt viros in coitu, iugulate:
Yanzu ku kashe dukan yara maza, ku kuma kashe kowace macen da ta yi lalata da namiji,
18 puellas autem et omnes feminas virgines reservate vobis:
amma ku bar kowace yarinyar da ba tă taɓa yin lalata da namiji ba.
19 et manete extra castra septem diebus. Qui occiderit hominem, vel occisum tetigerit, lustrabitur die tertio et septimo.
“Dukanku da kuka kashe mutum, ko kuka taɓa wani da aka kashe, dole ku kasance a bayan sansani har kwana bakwai. A rana ta uku da rana ta bakwai dole ku tsabtacce kanku da kuma bayinku.
20 Et de omni praeda, sive vestimentum fuerit, sive vas, et aliquid in utensilia praeparatum, de caprarum pellibus, et pilis, et ligno expiabitur.
Ku tsarkake kowace taguwa da kuma kome da aka yi da fata, da gashin akuya, ko kuwa itace.”
21 Eleazar quoque sacerdos ad viros exercitus, qui pugnaverunt, sic locutus est: Hoc est praeceptum legis, quod mandavit Dominus Moysi:
Sa’an nan Eleyazar firist, ya ce wa sojojin da suka je yaƙi, “Wannan ita ce ƙa’idar da Ubangiji ya ba wa Musa.
22 Aurum, et argentum, et aes, et ferrum, et plumbum, et stannum,
Zinariya, azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, kuza, darma
23 et omne, quod potest transire per flammas, igne purgabitur. quidquid autem ignem non potest sustinere, aqua expiationis sanctificabitur:
da dukan abin da wuta ba ta iya ci, dole yă shiga wuta sa’an nan zai zama da tsabta. Amma dole a kuma tsarkake ta da ruwan tsarkakewa. Duk abin da wuta za tă iya ci, dole a shigar da ita a ruwan tsarkakewa.
24 et lavabitis vestimenta vestra die septimo, et purificati postea castra intrabitis.
A rana ta bakwai za ku wanke tufafinku, sa’an nan za ku tsarkaka, bayan haka ku shigo sansani.”
25 Dixit quoque Dominus ad Moysen:
Ubangiji ya yi magana da Musa ya ce,
26 Tollite summam eorum, quae capta sunt ab homine usque ad pecus, tu et Eleazar sacerdos et principes vulgi:
“Da kai da Eleyazar firist, da shugabannin jama’a, ku ƙidaya dukan mutane da dabbobin da aka ci da yaƙi.
27 dividesque ex aequo praedam inter eos, qui pugnaverunt egressique sunt ad bellum, et inter omnem reliquam multitudinem.
Ku kasa ganimar kashi biyu, ku ba sojojin da suka tafi yaƙi kashi ɗaya, kashi ɗaya kuma ku ba wa jama’a.
28 et separabis partem Domino ab his, qui pugnaverunt et fuerunt in bello, unam animam de quingentis tam ex hominibus quam ex bobus et asinis et ovibus,
Daga sojojin da suka je yaƙin kuwa, ka ware ganima wa Ubangiji, ka ɗauki ɗaya daga cikin mutum ɗari biyar, da shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, da tumaki ɗari biyar.
29 et dabis eam Eleazaro sacerdoti, quia primitiae Domini sunt.
Ka ɗauki wannan sashe daga rabin rabonsu ka ba wa Eleyazar firist, a matsayin sashe na Ubangiji.
30 Ex media quoque parte filiorum Israel accipies quinquagesimum caput hominum, et boum, et asinorum, et ovium, cunctorum animantium, et dabis ea Levitis, qui excubant in custodiis tabernaculi Domini.
Daga cikin rabin rabon Isra’ilawa, ka zaɓi ɗaya daga kowane hamsin na mutane, shanu, jakuna, tumaki, awaki ko kuma sauran dabbobi. Ka ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.”
31 Feceruntque Moyses, et Eleazar, sicut praeceperat Dominus.
Saboda haka Musa da Eleyazar suka aikata yadda Ubangiji ya umarci Musa.
32 Fuit autem praeda, quam exercitus ceperat, ovium sexcenta septuaginta quinque millia,
Yawan ganimar da sojoji suka kawo ita ce tumaki 675,000
33 boum septuaginta duo millia,
shanu 72,000
34 asinorum sexaginta millia et mille:
da jakuna 61,000.
35 animae hominum sexus feminei, quae non cognoverant viros, triginta duo millia.
Akwai kuma mata 32,000 da ba su yi lalata ba da namiji ba.
36 Dataque est media pars his, qui in praelio fuerant, ovium trecenta triginta septem millia quingentae:
Kashin da aka ba sojoji waɗanda suka tafi yaƙi shi ne, tumaki 337,500,
37 e quibus in partem Domini supputatae sunt oves sexcentae septuaginta quinque.
tumakin da aka ware wa Ubangiji kuwa 657 ne;
38 Et de bobus triginta sex millibus, boves septuaginta et duo:
shanu 36,000, shanun da aka ware wa Ubangiji kuwa 72 ne;
39 de asinis triginta millibus quingentis, asini sexaginta unus:
jakuna 30,500, jakunan da aka ware wa Ubangiji kuwa 61 ne;
40 de animabus hominum sedecim millibus, cesserunt in partem Domini triginta duae animae.
mutane 16,000, mutanen da aka ware wa Ubangiji kuwa 32 ne.
41 Tradiditque Moyses numerum primitiarum Domini Eleazaro sacerdoti, sicut fuerat ei imperatum,
Musa ya ba wa Eleyazar abin da aka ware wa Ubangiji, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
42 ex media parte filiorum Israel, quam separaverat his, qui in praelio fuerant.
Kashin da aka ba wa Isra’ilawa, wanda Musa ya ware daga cikin na waɗanda suka tafi yaƙi,
43 De media vero parte, quae contigerat reliquae multitudini, id est, de ovibus trecentis triginta septem millibus quingentis,
kashin da aka ba wa jama’a kuwa tumaki 337,500 ne,
44 et de bobus triginta sex millibus,
shanu 36,000,
45 et de asinis triginta millibus quingentis,
jakuna 30,500
46 et de hominibus sedecim millibus,
da mutane 16,000.
47 tulit Moyses quinquagesimum caput, et dedit Levitis, qui excubabant in tabernaculo Domini, sicut praeceperat Dominus.
Daga rabin kashi na Isra’ilawa, Musa ya ɗauki ɗaya daga cikin hamsin na mutane da na dabbobi, yadda Ubangiji ya umarce shi, ya ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.
48 Cumque accessissent principes exercitus ad Moysen, et tribuni, centurionesque dixerunt:
Sai shugabannin da suka shugabancin rundunar yaƙin, shugabanni na dubu-dubu da shugabanni na ɗari-ɗari, suka zo wurin Musa
49 Nos servi tui recensuimus numerum pugnatorum, quos habuimus sub manu nostra: et ne unus quidem defuit.
suka ce masa, “Barorinka sun ƙidaya mayaƙan da suke ƙarƙashinmu, babu ko ɗayan ya ɓace.
50 Ob hanc causam offerimus in donariis Domini singuli quod in praeda auri potuimus invenire, periscelides et armillas, annulos et dextralia, ac muraenulas, ut depreceris pro nobis Dominum.
Saboda haka mun kawo wa Ubangiji hadaya na kayan zinariya da kowannenmu ya samu, mundaye, ƙawane,’yan kunne da duwatsun wuya, don yin wa kanmu kafara a gaban Ubangiji.”
51 Susceperuntque Moyses, et Eleazar sacerdos omne aurum in diversis speciebus,
Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya da kayan adon duka daga gare su.
52 pondo sedecim millia, septingentos quinquaginta siclos a tribunis et centurionibus.
Dukan zinariya da shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, waɗanda Musa da Eleyazar suka karɓa, suka kuma miƙa hadaya ga Ubangiji, nauyinta ta kai shekel 16,750.
53 Unusquisque enim quod in praeda rapuerat, suum erat.
Kowane soja, ya kwashi ganima wa kansa.
54 Et susceptum intulerunt in tabernaculum testimonii, in monimentum filiorum Israel coram Domino.
Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya daga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, suka kawo cikin Tentin Sujada, don su zama abin tuni ga Isra’ilawa a gaban Ubangiji.

< Liber Numeri 31 >