< Job 21 >
1 Respondens autem Iob, dixit:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Audite quaeso sermones meos, et agite poenitentiam.
“Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
3 Sustinete me, et ego loquar, et post mea, si videbitur, verba ridete.
Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
4 Numquid contra hominem disputatio mea est, ut merito non debeam contristari?
“A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
5 Attendite me, et obstupescite, et superponite digitum ori vestro:
Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
6 Et ego quando recordatus fuero, pertimesco, et concutit carnem meam tremor.
Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
7 Quare ergo impii vivunt, sublevati sunt, confortatique divitiis?
Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
8 Semen eorum permanet coram eis, propinquorum turba, et nepotum in conspectu eorum.
Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
9 Domus eorum securae sunt et pacatae, et non est virga Dei super illos.
Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
10 Bos eorum concepit, et non abortivit: vacca peperit, et non est privata foetu suo.
Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
11 Egrediuntur quasi greges parvuli eorum, et infantes eorum exultant lusibus.
Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
12 Tenent tympanum, et citharam, et gaudent ad sonitum organi.
Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
13 Ducunt in bonis dies suos, et in puncto ad inferna descendunt. (Sheol )
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol )
14 Qui dixerunt Deo: Recede a nobis, et scientiam viarum tuarum nolumus.
Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
15 Quis est Omnipotens, ut serviamus ei? et quid nobis prodest si oraverimus illum?
Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
16 Verumtamen quia non sunt in manu eorum bona sua, consilium impiorum longe sit a me.
Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
17 Quoties lucerna impiorum extinguetur, et superveniet eis inundatio, et dolores dividet furoris sui?
“Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
18 Erunt sicut paleae ante faciem venti, et sicut favilla quam turbo dispergit.
Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
19 Deus servabit filiis illius dolorem patris: et cum reddiderit, tunc sciet.
An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
20 Videbunt oculi eius interfectionem suam, et de furore Omnipotentis bibet.
Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
21 Quid enim ad eum pertinet de domo sua post se? et si numerus mensium eius dimidietur?
Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
22 Numquid Deus docebit quispiam scientiam, qui excelsos iudicat?
“Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
23 Iste moritur robustus et sanus, dives et felix.
Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
24 Viscera eius plena sunt adipe, et medullis ossa illius irrigantur:
jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
25 Alius vero moritur in amaritudine animae absque ullis opibus:
Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
26 Et tamen simul in pulvere dormient, et vermes operient eos.
Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
27 Certe novi cogitationes vestras, et sententias contra me iniquas.
“Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
28 Dicitis enim: Ubi est domus principis? et ubi tabernacula impiorum?
Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
29 Interrogate quemlibet de viatoribus, et haec eadem illum intelligere cognoscetis:
Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
30 Quia in diem perditionis servatur malus, et ad diem furoris ducetur.
cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
31 Quis arguet coram eo viam eius? et quae fecit, quis reddet illi?
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
32 Ipse ad sepulchra ducetur, et in congerie mortuorum vigilabit.
Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
33 Dulcis fuit glareis Cocyti, et post se omnem hominem trahet, et ante se innumerabiles.
Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
34 Quomodo igitur consolamini me frustra, cum responsio vestra repugnare ostensa sit veritati?
“Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”