< Psalmorum 72 >

1 Psalmus, in Salomonem.
Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
2 Deus, judicium tuum regi da, et justitiam tuam filio regis; judicare populum tuum in justitia, et pauperes tuos in judicio.
Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
3 Suscipiant montes pacem populo, et colles justitiam.
Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
4 Judicabit pauperes populi, et salvos faciet filios pauperum, et humiliabit calumniatorem.
Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
5 Et permanebit cum sole, et ante lunam, in generatione et generationem.
Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
6 Descendet sicut pluvia in vellus, et sicut stillicidia stillantia super terram.
Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
7 Orietur in diebus ejus justitia, et abundantia pacis, donec auferatur luna.
A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
8 Et dominabitur a mari usque ad mare, et a flumine usque ad terminos orbis terrarum.
Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
9 Coram illo procident Æthiopes, et inimici ejus terram lingent.
Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
10 Reges Tharsis et insulæ munera offerent; reges Arabum et Saba dona adducent:
Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
11 et adorabunt eum omnes reges terræ; omnes gentes servient ei.
Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
12 Quia liberabit pauperem a potente, et pauperem cui non erat adjutor.
Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
13 Parcet pauperi et inopi, et animas pauperum salvas faciet.
Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
14 Ex usuris et iniquitate redimet animas eorum, et honorabile nomen eorum coram illo.
Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
15 Et vivet, et dabitur ei de auro Arabiæ; et adorabunt de ipso semper, tota die benedicent ei.
Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
16 Et erit firmamentum in terra in summis montium; superextolletur super Libanum fructus ejus, et florebunt de civitate sicut fœnum terræ.
Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
17 Sit nomen ejus benedictum in sæcula; ante solem permanet nomen ejus. Et benedicentur in ipso omnes tribus terræ; omnes gentes magnificabunt eum.
Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
18 Benedictus Dominus Deus Israël, qui facit mirabilia solus.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
19 Et benedictum nomen majestatis ejus in æternum, et replebitur majestate ejus omnis terra. Fiat, fiat.
Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
20 Defecerunt laudes David, filii Jesse.
Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.

< Psalmorum 72 >