< Psalmorum 36 >

1 In finem. Servo Domini ipsi David. Dixit injustus ut delinquat in semetipso: non est timor Dei ante oculos ejus.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Akwai magana a cikin zuciyata game da zunubin mugu. Babu tsoron Allah a idanunsa.
2 Quoniam dolose egit in conspectu ejus, ut inveniatur iniquitas ejus ad odium.
Gama a idanunsa yana ganin kansa wani abu ne wanda ya sha ƙarfi a gane ko ya ƙi zunubinsa.
3 Verba oris ejus iniquitas, et dolus; noluit intelligere ut bene ageret.
Kalmomin bakinsa mugaye ne da kuma ruɗu; ya daina zama mai hikima da yin alheri.
4 Iniquitatem meditatus est in cubili suo; astitit omni viæ non bonæ: malitiam autem non odivit.
Ko a kan gadonsa ma yana shirya mugunta; yakan sa kansa ga aikata zunubi kuma ba ya ƙin abin da ba shi da kyau.
5 Domine, in cælo misericordia tua, et veritas tua usque ad nubes.
Ƙaunarka, ya Ubangiji, kan kai sammai, amincinka har sararin sammai.
6 Justitia tua sicut montes Dei; judicia tua abyssus multa. Homines et jumenta salvabis, Domine,
Adalcinka yana kama da manyan duwatsu, hukuncinka kamar zurfi mai girma. Ya Ubangiji, kana lura da mutum da dabba.
7 quemadmodum multiplicasti misericordiam tuam, Deus. Filii autem hominum in tegmine alarum tuarum sperabunt.
Ina misalin ƙaunarka marar ƙarewa! Mutane manya da ƙanana kan sami mafaka cikin inuwar fikafikanka.
8 Inebriabuntur ab ubertate domus tuæ, et torrente voluptatis tuæ potabis eos:
Suna biki a yalwar gidanka; kakan ba su sha daga rafin farin cikinka.
9 quoniam apud te est fons vitæ, et in lumine tuo videbimus lumen.
Gama a gare ka akwai maɓulɓular rai cikin haskenka mukan ga haske.
10 Prætende misericordiam tuam scientibus te, et justitiam tuam his qui recto sunt corde.
Ka ci gaba da ƙaunarka ga waɗanda suka san ka, adalcinka ga masu gaskiyar zuciya.
11 Non veniat mihi pes superbiæ, et manus peccatoris non moveat me.
Kada ka bari ƙafar mai girman kai yă fāɗa mini, ko hannun mugu ya kore ni.
12 Ibi ceciderunt qui operantur iniquitatem; expulsi sunt, nec potuerunt stare.
Dubi yadda masu aikata zunubi suka fāɗi, a zube, ba za su kuwa iya tashi ba!

< Psalmorum 36 >