< Psalmorum 17 >

1 Oratio David. Exaudi, Domine, justitiam meam; intende deprecationem meam. Auribus percipe orationem meam, non in labiis dolosis.
Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
2 De vultu tuo judicium meum prodeat; oculi tui videant æquitates.
Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
3 Probasti cor meum, et visitasti nocte; igne me examinasti, et non est inventa in me iniquitas.
Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
4 Ut non loquatur os meum opera hominum: propter verba labiorum tuorum, ego custodivi vias duras.
Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
5 Perfice gressus meos in semitis tuis, ut non moveantur vestigia mea.
Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
6 Ego clamavi, quoniam exaudisti me, Deus; inclina aurem tuam mihi, et exaudi verba mea.
Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
7 Mirifica misericordias tuas, qui salvos facis sperantes in te.
Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
8 A resistentibus dexteræ tuæ custodi me ut pupillam oculi. Sub umbra alarum tuarum protege me
Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
9 a facie impiorum qui me afflixerunt. Inimici mei animam meam circumdederunt;
daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
10 adipem suum concluserunt: os eorum locutum est superbiam.
Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
11 Projicientes me nunc circumdederunt me; oculos suos statuerunt declinare in terram.
Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
12 Susceperunt me sicut leo paratus ad prædam, et sicut catulus leonis habitans in abditis.
Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
13 Exsurge, Domine: præveni eum, et supplanta eum: eripe animam meam ab impio; frameam tuam
Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
14 ab inimicis manus tuæ. Domine, a paucis de terra divide eos in vita eorum; de absconditis tuis adimpletus est venter eorum. Saturati sunt filiis, et dimiserunt reliquias suas parvulis suis.
Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
15 Ego autem in justitia apparebo conspectui tuo; satiabor cum apparuerit gloria tua.
Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.

< Psalmorum 17 >