< Lamentationes 3 >

1 Ego vir videns paupertatem meam in virga indignationis ejus.
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 Me minavit, et adduxit in tenebras, et non in lucem.
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 Tantum in me vertit et convertit manum suam tota die.
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 Vetustam fecit pellem meam et carnem meam; contrivit ossa mea.
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 Ædificavit in gyro meo, et circumdedit me felle et labore.
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 In tenebrosis collocavit me, quasi mortuos sempiternos.
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 Circumædificavit adversum me, ut non egrediar; aggravavit compedem meum.
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 Sed et cum clamavero, et rogavero, exclusit orationem meam.
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 Conclusit vias meas lapidibus quadris; semitas meas subvertit.
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 Ursus insidians factus est mihi, leo in absconditis.
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 Semitas meas subvertit, et confregit me; posuit me desolatam.
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 Tetendit arcum suum, et posuit me quasi signum ad sagittam.
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 Misit in renibus meis filias pharetræ suæ.
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 Factus sum in derisum omni populo meo, canticum eorum tota die.
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 Replevit me amaritudinibus; inebriavit me absinthio.
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 Et fregit ad numerum dentes meos; cibavit me cinere.
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 Et repulsa est a pace anima mea; oblitus sum bonorum.
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 Et dixi: Periit finis meus, et spes mea a Domino.
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 Recordare paupertatis, et transgressionis meæ, absinthii et fellis.
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 Memoria memor ero, et tabescet in me anima mea.
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 Hæc recolens in corde meo, ideo sperabo.
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 Misericordiæ Domini, quia non sumus consumpti; quia non defecerunt miserationes ejus.
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 Novi diluculo, multa est fides tua.
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 Pars mea Dominus, dixit anima mea; propterea exspectabo eum.
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 Bonus est Dominus sperantibus in eum, animæ quærenti illum.
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 Bonum est præstolari cum silentio salutare Dei.
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 Bonum est viro cum portaverit jugum ab adolescentia sua.
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 Sedebit solitarius, et tacebit, quia levavit super se.
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29 Ponet in pulvere os suum, si forte sit spes.
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 Dabit percutienti se maxillam: saturabitur opprobriis.
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 Quia non repellet in sempiternum Dominus.
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 Quia si abjecit, et miserebitur, secundum multitudinem misericordiarum suarum.
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 Non enim humiliavit ex corde suo et abjecit filios hominum.
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 Ut conteret sub pedibus suis omnes vinctos terræ.
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 Ut declinaret judicium viri in conspectu vultus Altissimi.
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 Ut perverteret hominem in judicio suo; Dominus ignoravit.
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 Quis est iste qui dixit ut fieret, Domino non jubente?
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 Ex ore Altissimi non egredientur nec mala nec bona?
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 Quid murmuravit homo vivens, vir pro peccatis suis?
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 Scrutemur vias nostras, et quæramus, et revertamur ad Dominum.
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 Levemus corda nostra cum manibus ad Dominum in cælos.
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 Nos inique egimus, et ad iracundiam provocavimus; idcirco tu inexorabilis es.
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 Operuisti in furore, et percussisti nos; occidisti, nec pepercisti.
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 Opposuisti nubem tibi, ne transeat oratio.
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 Eradicationem et abjectionem posuisti me in medio populorum.
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 Aperuerunt super nos os suum omnes inimici.
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 Formido et laqueus facta est nobis vaticinatio, et contritio.
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 Divisiones aquarum deduxit oculus meus, in contritione filiæ populi mei.
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 Oculus meus afflictus est, nec tacuit, eo quod non esset requies.
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 Donec respiceret et videret Dominus de cælis.
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 Oculus meus deprædatus est animam meam in cunctis filiabus urbis meæ.
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 Venatione ceperunt me quasi avem inimici mei gratis.
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 Lapsa est in lacum vita mea, et posuerunt lapidem super me.
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 Inundaverunt aquæ super caput meum; dixi: Perii.
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 Invocavi nomen tuum, Domine, de lacu novissimo.
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 Vocem meam audisti; ne avertas aurem tuam a singultu meo et clamoribus.
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 Appropinquasti in die quando invocavi te; dixisti: Ne timeas.
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 Judicasti, Domine, causam animæ meæ, redemptor vitæ meæ.
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 Vidisti, Domine, iniquitatem illorum adversum me: judica judicium meum.
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 Vidisti omnem furorem, universas cogitationes eorum adversum me.
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 Audisti opprobrium eorum, Domine, omnes cogitationes eorum adversum me.
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 Labia insurgentium mihi, et meditationes eorum adversum me tota die.
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 Sessionem eorum et resurrectionem eorum vide; ego sum psalmus eorum.
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 Redes eis vicem, Domine, juxta opera manuum suarum.
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 Dabis eis scutum cordis, laborem tuum.
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 Persequeris in furore, et conteres eos sub cælis, Domine.
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.

< Lamentationes 3 >