< Job 33 >

1 Audi igitur, Job, eloquia mea, et omnes sermones meos ausculta.
“Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
2 Ecce aperui os meum: loquatur lingua mea in faucibus meis.
Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
3 Simplici corde meo sermones mei, et sententiam puram labia mea loquentur.
Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
4 Spiritus Dei fecit me, et spiraculum Omnipotentis vivificavit me.
Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
5 Si potes, responde mihi, et adversus faciem meam consiste.
Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
6 Ecce, et me sicut et te fecit Deus, et de eodem luto ego quoque formatus sum.
Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
7 Verumtamen miraculum meum non te terreat, et eloquentia mea non sit tibi gravis.
Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
8 Dixisti ergo in auribus meis, et vocem verborum tuorum audivi:
“Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
9 Mundus sum ego, et absque delicto: immaculatus, et non est iniquitas in me.
‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
10 Quia querelas in me reperit, ideo arbitratus est me inimicum sibi.
Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
11 Posuit in nervo pedes meos; custodivit omnes semitas meas.
ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
12 Hoc est ergo in quo non es justificatus: respondebo tibi, quia major sit Deus homine.
“Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
13 Adversus eum contendis, quod non ad omnia verba responderit tibi?
Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
14 Semel loquitur Deus, et secundo idipsum non repetit.
Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
15 Per somnium, in visione nocturna, quando irruit sopor super homines, et dormiunt in lectulo,
A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
16 tunc aperit aures virorum, et erudiens eos instruit disciplina,
mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
17 ut avertat hominem ab his quæ facit, et liberet eum de superbia,
don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
18 eruens animam ejus a corruptione, et vitam illius ut non transeat in gladium.
don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
19 Increpat quoque per dolorem in lectulo, et omnia ossa ejus marcescere facit.
“Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
20 Abominabilis ei fit in vita sua panis, et animæ illius cibus ante desiderabilis.
yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
21 Tabescet caro ejus, et ossa, quæ tecta fuerant, nudabuntur.
Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
22 Appropinquavit corruptioni anima ejus, et vita illius mortiferis.
Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
23 Si fuerit pro eo angelus loquens, unus de millibus, ut annuntiet hominis æquitatem,
Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
24 miserebitur ejus, et dicet: Libera eum, ut non descendat in corruptionem: inveni in quo ei propitier.
yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
25 Consumpta est caro ejus a suppliciis: revertatur ad dies adolescentiæ suæ.
Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
26 Deprecabitur Deum, et placabilis ei erit: et videbit faciem ejus in jubilo, et reddet homini justitiam suam.
Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
27 Respiciet homines, et dicet: Peccavi, et vere deliqui, et ut eram dignus, non recepi.
Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
28 Liberavit animam suam, ne pergeret in interitum, sed vivens lucem videret.
Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
29 Ecce hæc omnia operatur Deus tribus vicibus per singulos,
“Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
30 ut revocet animas eorum a corruptione, et illuminet luce viventium.
Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
31 Attende, Job, et audi me: et tace, dum ego loquor.
“Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
32 Si autem habes quod loquaris, responde mihi: loquere, volo enim te apparere justum.
In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
33 Quod si non habes, audi me: tace, et docebo te sapientiam.
Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”

< Job 33 >