< Psalmorum 92 >
1 Psalmus Cantici, In die sabbati. Bonum est confiteri Domino: et psallere nomini tuo Altissime.
Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
2 Ad annunciandum mane misericordiam tuam: et veritatem tuam per noctem.
don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
3 In decachordo, psalterio: cum cantico, in cithara.
da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
4 Quia delectasti me Domine in factura tua: et in operibus manuum tuarum exultabo.
Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
5 Quam magnificata sunt opera tua Domine! nimis profundæ factæ sunt cogitationes tuæ:
Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
6 Vir insipiens non cognoscet: et stultus non intelliget hæc.
Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
7 Cum exorti fuerint peccatores sicut fœnum: et apparuerint omnes, qui operantur iniquitatem: Ut intereant in sæculum sæculi:
cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
8 tu autem Altissimus in æternum Domine.
Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
9 Quoniam ecce inimici tui Domine, quoniam ecce inimici tui peribunt: et dispergentur omnes, qui operantur iniquitatem.
Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
10 Et exaltabitur sicut unicornis cornu meum: et senectus mea in misericordia uberi.
Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
11 Et despexit oculus meus inimicos meos: et in insurgentibus in me malignantibus audiet auris mea.
Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
12 Iustus ut palma florebit: sicut cedrus Libani multiplicabitur.
Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
13 Plantati in domo Domini, in atriis domus Dei nostri florebunt.
da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
14 Adhuc multiplicabuntur in senecta uberi: et bene patientes erunt,
Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
15 ut annuncient: Quoniam rectus Dominus Deus noster: et non est iniquitas in eo.
suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”