< Psalmorum 108 >
1 Canticum Psalmi ipsi David. Paratum cor meum Deus, paratum cor meum: cantabo, et psallam in gloria mea.
Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
2 Exurge gloria mea, exurge psalterium, et cithara: exurgam diluculo.
Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
3 Confitebor tibi in populis Domine: et psallam tibi in nationibus.
Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
4 Quia magna est super cælos misericordia tua: et usque ad nubes veritas tua:
Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
5 Exaltare super cælos Deus, et super omnem terram gloria tua:
A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
6 ut liberentur dilecti tui. Salvum fac dextera tua, et exaudi me:
Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
7 Deus locutus est in sancto suo: Exultabo, et dividam Sichimam, et convallem tabernaculorum dimetiar.
Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
8 Meus est Galaad, et meus est Manasses: et Ephraim susceptio capitis mei. Iuda rex meus:
Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
9 Moab lebes spei meæ. In Idumæam extendam calceamentum meum: mihi alienigenæ amici facti sunt.
Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
10 Quis deducet me in civitatem munitam? quis deducet me usque in Idumæam?
Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
11 Nonne tu Deus, qui repulisti nos, et non exibis Deus in virtutibus nostris?
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
12 Da nobis auxilium de tribulatione: quia vana salus hominis.
Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
13 In Deo faciemus virtutem: et ipse ad nihilum deducet inimicos nostros.
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.