< Job 13 >

1 Ecce omnia hæc vidit oculus meus, et audivit auris mea, et intellexi singula.
“Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
2 Secundum scientiam vestram et ego novi: nec inferior vestri sum.
Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
3 Sed tamen ad Omnipotentem loquar, et disputare cum Deo cupio:
Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
4 Prius vos ostendens fabricatores mendacii, et cultores perversorum dogmatum.
Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
5 Atque utinam taceretis, ut putaremini esse sapientes.
In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
6 Audite ergo correptionem meam, et iudicium labiorum meorum attendite.
Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
7 Numquid Deus indiget vestro mendacio, ut pro illo loquamini dolos?
Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
8 Numquid faciem eius accipitis, et pro Deo iudicare nitimini?
Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
9 Aut placebit ei quem celare nihil potest? aut decipietur ut homo, vestris fraudulentiis?
In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
10 Ipse vos arguet, quoniam in abscondito faciem eius accipitis.
Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
11 Statim ut se commoverit, turbabit vos, et terror eius irruet super vos.
Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
12 Memoria vestra comparabitur cineri, et redigentur in lutum cervices vestræ.
Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
13 Tacete paulisper ut loquar quodcumque mihi mens suggesserit.
“Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
14 Quare lacero carnes meas dentibus meis, et animam meam porto in manibus meis?
Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
15 Etiam si occiderit me, in ipso sperabo: verumtamen vias meas in conspectu eius arguam.
Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
16 Et ipse erit salvator meus: non enim veniet in conspectu eius omnis hypocrita.
lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
17 Audite sermonem meum, et ænigmata percipite auribus vestris.
Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
18 Si fuero iudicatus, scio quod iustus inveniar.
Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
19 Quis est qui iudicetur mecum? veniat: quare tacens consumor?
Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
20 Duo tantum ne facias mihi, et tunc a facie tua non abscondar:
“Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
21 Manum tuam longe fac a me, et formido tua non me terreat.
Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
22 Voca me, et ego respondebo tibi: aut certe loquar, et tu responde mihi.
Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
23 Quantas habeo iniquitates et peccata, scelera mea et delicta ostende mihi.
Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
24 Cur faciem tuam abscondis, et arbitraris me inimicum tuum?
Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
25 Contra folium, quod vento rapitur, ostendis potentiam tuam, et stipulam siccam persequeris:
Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
26 Scribis enim contra me amaritudines, et consumere me vis peccatis adolescentiæ meæ.
Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
27 Posuisti in nervo pedem meum, et observasti omnes semitas meas, et vestigia pedum meorum considerasti:
Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
28 Qui quasi putredo consumendus sum, et quasi vestimentum quod comeditur a tinea.
“Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.

< Job 13 >