< Job 34 >

1 Pronuntians itaque Eliu, etiam hæc locutus est:
Sa’an nan Elihu ya ce,
2 [Audite, sapientes, verba mea: et eruditi, auscultate me.
“Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
3 Auris enim verba probat, et guttur escas gustu dijudicat.
Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
4 Judicium eligamus nobis, et inter nos videamus quid sit melius.
Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
5 Quia dixit Job: Justus sum, et Deus subvertit judicium meum.
“Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
6 In judicando enim me mendacium est: violenta sagitta mea absque ullo peccato.
Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
7 Quis est vir ut est Job, qui bibit subsannationem quasi aquam:
Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
8 qui graditur cum operantibus iniquitatem, et ambulat cum viris impiis?
Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
9 Dixit enim: Non placebit vir Deo, etiam si cucurrerit cum eo.
Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
10 Ideo, viri cordati, audite me: absit a Deo impietas, et ab Omnipotente iniquitas.
“Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
11 Opus enim hominis reddet ei, et juxta vias singulorum restituet eis.
Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
12 Vere enim Deus non condemnabit frustra, nec Omnipotens subvertet judicium.
Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
13 Quem constituit alium super terram? aut quem posuit super orbem quem fabricatus est?
Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
14 Si direxerit ad eum cor suum, spiritum illius et flatum ad se trahet.
In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
15 Deficiet omnis caro simul, et homo in cinerem revertetur.
’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
16 Si habes ergo intellectum, audi quod dicitur, et ausculta vocem eloquii mei:
“In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
17 numquid qui non amat judicium sanari potest? et quomodo tu eum qui justus est in tantum condemnas?
Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
18 Qui dicit regi: Apostata; qui vocat duces impios;
Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
19 qui non accipit personas principum, nec cognovit tyrannum cum disceptaret contra pauperem: opus enim manuum ejus sunt universi.
wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
20 Subito morientur, et in media nocte turbabuntur populi: et pertransibunt, et auferent violentum absque manu.
Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
21 Oculi enim ejus super vias hominum, et omnes gressus eorum considerat.
“Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
22 Non sunt tenebræ, et non est umbra mortis, ut abscondantur ibi qui operantur iniquitatem,
Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
23 neque enim ultra in hominis potestate est, ut veniat ad Deum in judicium.
Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
24 Conteret multos, et innumerabiles, et stare faciet alios pro eis.
Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
25 Novit enim opera eorum, et idcirco inducet noctem, et conterentur.
Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
26 Quasi impios percussit eos in loco videntium:
Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
27 qui quasi de industria recesserunt ab eo, et omnes vias ejus intelligere noluerunt:
domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
28 ut pervenire facerent ad eum clamorem egeni, et audiret vocem pauperum.
Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
29 Ipso enim concedente pacem, quis est qui condemnet? ex quo absconderit vultum, quis est qui contempletur eum, et super gentes, et super omnes homines?
Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
30 Qui regnare facit hominem hypocritam propter peccata populi.
yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
31 Quia ergo ego locutus sum ad Deum, te quoque non prohibebo.
“A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
32 Si erravi, tu doce me; si iniquitatem locutus sum, ultra non addam.
Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
33 Numquid a te Deus expetit eam, quia displicuit tibi? tu enim cœpisti loqui, et non ego: quod si quid nosti melius, loquere.
Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
34 Viri intelligentes loquantur mihi, et vir sapiens audiat me.
“Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
35 Job autem stulte locutus est, et verba illius non sonant disciplinam.
‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
36 Pater mi, probetur Job usque ad finem: ne desinas ab homine iniquitatis:
Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
37 quia addit super peccata sua blasphemiam, inter nos interim constringatur: et tunc ad judicium provocet sermonibus suis Deum.]
Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”

< Job 34 >