< Job 16 >

1 Respondens autem Job, dixit:
Sai Ayuba ya amsa,
2 [Audivi frequenter talia: consolatores onerosi omnes vos estis.
“Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
3 Numquid habebunt finem verba ventosa? aut aliquid tibi molestum est, si loquaris?
Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
4 Poteram et ego similia vestri loqui, atque utinam esset anima vestra pro anima mea: consolarer et ego vos sermonibus, et moverem caput meum super vos;
Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
5 roborarem vos ore meo, et moverem labia mea, quasi parcens vobis.
Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
6 Sed quid agam? Si locutus fuero, non quiescet dolor meus, et si tacuero, non recedet a me.
“Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
7 Nunc autem oppressit me dolor meus, et in nihilum redacti sunt omnes artus mei.
Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
8 Rugæ meæ testimonium dicunt contra me, et suscitatur falsiloquus adversus faciem meam, contradicens mihi.
Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
9 Collegit furorem suum in me, et comminans mihi, infremuit contra me dentibus suis: hostis meus terribilibus oculis me intuitus est.
Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
10 Aperuerunt super me ora sua, et exprobrantes percusserunt maxillam meam: satiati sunt pœnis meis.
Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
11 Conclusit me Deus apud iniquum, et manibus impiorum me tradidit.
Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
12 Ego ille quondam opulentus, repente contritus sum: tenuit cervicem meam, confregit me, et posuit me sibi quasi in signum.
Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
13 Circumdedit me lanceis suis; convulneravit lumbos meos: non pepercit, et effudit in terra viscera mea.
maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
14 Concidit me vulnere super vulnus: irruit in me quasi gigas.
Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
15 Saccum consui super cutem meam, et operui cinere carnem meam.
“Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
16 Facies mea intumuit a fletu, et palpebræ meæ caligaverunt.
Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
17 Hæc passus sum absque iniquitate manus meæ, cum haberem mundas ad Deum preces.
duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
18 Terra, ne operias sanguinem meum, neque inveniat in te locum latendi clamor meus:
“Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
19 ecce enim in cælo testis meus, et conscius meus in excelsis.
Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
20 Verbosi amici mei: ad Deum stillat oculus meus:
Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
21 atque utinam sic judicaretur vir cum Deo, quomodo judicatur filius hominis cum collega suo.
a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
22 Ecce enim breves anni transeunt, et semitam per quam non revertar ambulo.]
“Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.

< Job 16 >