< زەبوورەکان 73 >
زەبوورێکی ئاساف. بێگومان خودا چاکە بۆ ئیسرائیل، بۆ دڵپاکەکان. | 1 |
Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
بەڵام من خەریک بوو پێم بخزێت و زۆری نەمابوو هەنگاوم بخلیسکێت، | 2 |
Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
چونکە بەغیلیم بە لووتبەرزەکان برد، کە ئاسوودەیی بەدکارانم دی. | 3 |
Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
ترسیان لە مردن نییە، جەستەیان تەندروست و قەڵەوە. | 4 |
Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
لە ڕەنجکێشانی مرۆڤ بەدەرن، وەک خەڵکی تێناکەون. | 5 |
Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
بۆیە لووتبەرزییان وەک ملوانکە لە مل کردووە و بەرگی توندوتیژییان پۆشیوە. | 6 |
Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
خراپە لە دڵی بێ بەزەییانەوە دێت، لێکدانەوەی دڵیان بێ سنوورە. | 7 |
Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
گاڵتەجاڕی دەکەن و بە خراپە دەدوێن، بە لووتبەرزییەوە باسی ستەم دەکەن. | 8 |
Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
ڕووی دەمیان لە ئاسمان کردووە، زمانیشیان بەسەر زەویدا دەگێڕن. | 9 |
Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
بۆیە خەڵکی خۆیان دێنە لایان و باوەڕ بە قسەکانیان دەکەن. | 10 |
Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
دەڵێن: «چۆن خودا دەزانێت؟ ئایا لەلای هەرەبەرز زانیاری هەیە؟» | 11 |
Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
ئەوەتا ئەمانە بەدکارن، هەمیشە لە خۆشیدان و سامانیان لە زیادبووندایە. | 12 |
Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
بێگومان بە بێهوودە دڵی خۆمم بە پاکی ڕاگرتووە، دەستیشم بە بێگەردی شوشتووە. | 13 |
Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
بە درێژایی ڕۆژ لێم قەومابوو، هەتا بەرەبەیان تەمبێ کرابووم. | 14 |
Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
ئەگەر بە ڕاشکاوی قسەم دەکرد، ئەوا لەگەڵ منداڵەکانت ناپاک دەبووم. | 15 |
Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
کاتێک ویستم لەمە تێبگەم، بە ئەرکێکی سەختم بینی، | 16 |
Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
هەتا چوومە ناو پیرۆزگای خودا، ئەوسا لە چارەنووسیان تێگەیشتم. | 17 |
sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
بە ڕاستی لە جێگایەکی خلیسک داتناون، تووشی وێرانیت کردوون. | 18 |
Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
چۆن بە چاوتروکانێک وێران بوون، لە ترسان بە تەواوی لەناوچوون! | 19 |
Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
ئەی پەروەردگار، وەک خەون کاتی بەئاگا هاتنەوە، لە کاتی بەئاگایی وەک خەون ڕیسوایان دەکەیت. | 20 |
Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
کاتێک دڵم تەنگ بوو، وەک شمشێر هەناومی بڕی، | 21 |
Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
گێل و نەزان بووم، لەلای تۆ وەک ئاژەڵم لێهات. | 22 |
na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
لەگەڵ ئەوەشدا، من هەمیشە لەلای تۆم، دەستی ڕاستی منت گرت. | 23 |
Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
بە ئامۆژگاریت ڕێنماییم دەکەیت، پاشان بۆ شکۆمەندیم دەبەیت. | 24 |
Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
بێجگە لە تۆ لە ئاسمان کێم هەیە؟ ئەگەر لەگەڵ تۆ بم، لەسەر زەویش هیچ نییە ئارەزووی بکەم. | 25 |
Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
جەسته و دڵم کۆتاییان پێدێت، بەڵام هەتاهەتایە هێزی دڵ و بەشی من خودایە. | 26 |
Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
ئەوەتا ئەوانەی لە تۆ دوورن وێڵ دەبن، ئەوانەی ناپاکیت لەگەڵ بکەن دوایان دەبڕیتەوە. | 27 |
Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
بەڵام نزیکبوونەوە لە خودا بۆ من باشە، یەزدانی باڵادەستم کرد بە پەناگام، هەتا باسی هەموو کردەوەکانت بکەم. | 28 |
Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.