< ئەیوب 33 >
«بەڵام ئەی ئەیوب، ئێستا گوێ لە قسەکانم بگرە! گوێ شل بکە بۆ هەموو وشەکانم. | 1 |
“Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
ئەوەتا من دەمم کردەوە؛ قسەکانم لەسەر زمانی منن. | 2 |
Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
قسەکانم لە دڵی پاکمەوەن؛ زمانیشم بە دڵسۆزییەوە ئەوە دەردەبڕێت کە دەیزانم. | 3 |
Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
ڕۆحی خودا دروستی کردم، هەناسەی توانادارەکە ژیانی پێ بەخشیم. | 4 |
Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
ئەگەر دەتوانیت، وەڵامم بدەوە و هەستە سەرپێ و کێشەکەت بخەرە بەردەمم. | 5 |
Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
لەبەرچاوی خودا منیش هەروەکو تۆم، لە قوڕ دروستکراوم. | 6 |
Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
ناشێت شەوکەتم بتترسێنێت و زۆرکردنم لێت بارت گران بکات. | 7 |
Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
«تۆ لەبەردەمم گوتت، من بە وردی گوێم لێت بوو، | 8 |
“Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
گوتت:”من بێتاوانم بەبێ یاخیبوون، بێگەردم و تاوانم نییە. | 9 |
‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
لەگەڵ ئەوەشدا خودا دەگەڕێت هەڵەم لێ بدۆزێتەوە و بە دوژمنی خۆی دامدەنێت. | 10 |
Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
پێیەکانمی لەناو کۆت داناوە؛ چاودێری هەموو ڕێگاکانم دەکات.“ | 11 |
ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
«بەڵام پێتان دەڵێم، لەمەدا ڕاست ناکەیت، چونکە خودا لە مرۆڤ مەزنترە. | 12 |
“Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
بۆچی سکاڵای لێ دەکەیت:”وەڵامی هیچ کام لە وشەکانی مرۆڤ ناداتەوە؟“ | 13 |
Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
بە ڕاستی خودا هەرجارەو بە ڕێگایەک دەدوێت، کەس ڕامانی ئەوە ناکات. | 14 |
Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
لە خەون، لە بینینی شەودا، کاتێک هەموو خەڵک خەوی قورسیان لێدەکەوێت لە کاتی خەواڵووبوون لەناو جێگا، | 15 |
A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
ئەو کاتە گوێی خەڵک دەکاتەوە و بە ئاگادارکردنەوەکانی دەیانتۆقێنێت، | 16 |
mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
تاکو لە خراپەکردن بیانگەڕێنێتەوە و لە لووتبەرزیش بیانپارێزێت، | 17 |
don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
هەتا لە کەوتنە ناو گۆڕ ڕزگاریان بکات، ژیانیشیان لە لەناوچوون بە شمشێر. | 18 |
don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
«یان ئەگەر کەسێکی هەبێت لەناو جێگاکەی بە ئازار تەمبێ بکرێت و ململانێی ئێسکەکانیشی بەردەوامە، | 19 |
“Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
ئەو کاتە گیانی ڕقی لە نان دەبێتەوە و نەوسیشی لە خواردنی خۆش. | 20 |
yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
گۆشتیان وا دەفەوتێت کە ئیتر نەبینرێت، ئێسکەکانیشیان کە شاردرابوونەوە ئێستا دیارن. | 21 |
Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
گیانیان لە گۆڕ نزیک دەبنەوە، ژیانیشیان لە فریشتەی مەرگ. | 22 |
Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
لەگەڵ ئەوەشدا ئەگەر لەلایان نێردراوێک هەبێت، پەیوەندی ڕێکخەرێک، یەک لە هەزار تاکو ڕاستودروستی بە مرۆڤ بناسێنێت، | 23 |
Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
لەگەڵ ئەو کەسە میهرەبان دەبێت و بە خودا دەڵێت:”بیانگەڕێنەوە با نەکەونە گۆڕ؛ کڕینەوەی ژیانی ئەوانم بۆ دۆزینەوە. | 24 |
yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
با گۆشتیان لە گۆشتی منداڵ ناسکتر بێت؛ با ڕۆژانی گەنجیێتییان بگەڕێتەوە.“ | 25 |
Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
ئەو کاتە ئەوانە داوا لە خودا دەکەن و لێیان ڕازی دەبێت، بە هاواری خۆشییەوە ڕووی خودا دەبینن، ئەویش پاداشتی ڕاستودروستی مرۆڤ دەداتەوە. | 26 |
Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
دەچن بۆ لای کەسانی دیکە و دەڵێن:”گوناهم کرد و ڕاستیم خواروخێچ کرد، بەڵام سزا نەدرام لەسەری. | 27 |
Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
خودا منی کڕییەوە لە جیهانی مردووان، ئیتر ژیانم ڕووناکی دەبینێت.“ | 28 |
Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
«خودا هەموو ئەمانە دەکات، دوو جار و سێ جار لەگەڵ مرۆڤ، | 29 |
“Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
بۆ ئەوەی بیانگەڕێنێتەوە لە کەوتنی ناو گۆڕ و تاوەکو بە ڕووناکی زیندووان ڕووناک بێتەوە. | 30 |
Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
«جا گوێ شل بکە و گوێم لێ بگرە ئەیوب! بێدەنگ بە من قسە دەکەم. | 31 |
“Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
ئەگەر قسەت لەلایە وەڵامم بدەوە، قسە بکە! چونکە دەمەوێت ئەستۆپاکت بکەم. | 32 |
In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
ئەگەر نا، تۆ گوێم لێ بگرە؛ بێدەنگ بە فێری داناییت دەکەم.» | 33 |
Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”