< Johani 6 >
1 Hazimana inzi zintu, Jesu chayenda kuyimwi imbali ye wate lya Galileya, hape livali kusupiwa I wate lya Tiberiya.
Ɗan lokaci bayan wannan, sai Yesu ya ƙetare zuwa gaɓar mai nesa na Tekun Galili (wato, Tekun Tibariya),
2 Vungi vwe chichava chivali kumwi chilire kakuli vava voni imakazo zavali kupanga kwavo vavali kulwala.
sai taro mai yawa na mutane suka bi shi domin sun ga abubuwan banmamakin da ya yi ga marasa lafiya.
3 Jesu cha yenda kwirundu mi uko abake kali hasi ni varutwana vakwe.
Sa’an nan Yesu ya hau gefen dutse ya zauna tare da almajiransa.
4 (Hanu mukiti we Paseka, Mukiti wa Majunda, uvali kwina hafuhi.)
Bikin Ƙetarewan Yahudawa ya yi kusa.
5 Linu Jesu halola mwi wulu ni kuvona vantu vangi niva keza kwakwe, cha wambira Filipi, “Tuwola kuwula kuhi vuronto ili kuli ava vantu va wole kulya?”
Sa’ad da Yesu ya ɗaga kai ya ga taro mai yawa suna zuwa wajensa, sai ya ce wa Filibus, “Ina za mu sayi burodi saboda mutanen nan su ci?”
6 (Kono Jesu a vawambi ichi kulika Filipi, kakuli iye mwine ivali kwizi icho chavali kuswanera kupanga.)
Ya yi wannan tambayar don yă gwada shi ne kawai, gama ya riga ya san abin da zai yi.
7 Filipi cha mwi tava, “Miyanda yovere yamashereñi ovuroto kasa a wole kuwulira zumwi ni zumwi wavo nangati kakwa kanini.”
Sai Filibus ya amsa ya ce, “Kai, ko albashin wata takwas ba zai iya sayan isashen burodin da kowa zai ɗan samu kaɗan ba!”
8 Zumwi wa valutwana vakwe, Adiriyasi, mukulwe wa Simoni Pita, chata kwa Jesu,
Sai wani daga cikin almajiransa Andarawus, ɗan’uwan Bitrus, ya yi magana,
9 “Kwina muhwire wo muswisu hanu wina zikwa zeminwe ye yanza zo Vuroto ni nswi zo vere, kono chinzi ichi mukati ketu?”
“Ga wani yaro da ƙananan burodin sha’ir guda biyar da ƙananan kifi biyu, amma me wannan zai yi wa yawan mutanen nan.”
10 Jesu chati, “Mwikalike vantu hansi.”( Hanu kuvena lyani liñgi mwe china chivaka, ) Cwale vakwame chive kala hansi, valikana lule na lule lwe minwe yeyanza ku mpalo.
Yesu ya ce, “Ku sa mutanen su zauna.” Wurin kuwa akwai ciyawa da sosai, sai maza suka zazzauna, sun kai wajen dubu biyar.
11 Linu Jesu chahinda vuloto mi hamana kuha vuitumero, cha tambika kwavo vavali kwi kere, mi kuswana nikwi inswi, chovungi sina muvavali kusakira.
Sa’an nan Yesu ya ɗauki burodin, ya yi godiya, ya kuma rarraba wa waɗanda suke zaune gwargwadon abin da ya ishe su. Haka kuma ya yi da kifin.
12 Linu vantu havave kuti, cha wamba kuva lutwana vakwe, “Mukunganye vu fwafwali ni twa ngamoka twa shala, iri kuli kanji kuwaniki chi zova.”
Sa’ad da duk suka ci suka ƙoshi, sai ya ce wa almajiransa, “Ku tattara gutsattsarin da suka rage. Kada kome yă lalace.”
13 Chale chiva tu kunganya ni kwizuza zitanda ze kumi ni tovere tufwafwali tuva zwi ha vuronto bwina palo ye minwe ye yanza ye; tu fwafwali tuva shali kwavo vavali.
Saboda haka suka tattara su suka kuma cika kwanduna goma sha biyu na gutsattsarin burodin sha’ir biyar nan da suka ragu bayan kowa ya ci.
14 Linu, vantu hava vona ichi chisupo chava pangi, chiva wamba, “Uzu chovu niti muporofita yo swanera kukeza mwi nkanda.”
Bayan mutanen suka ga abin banmamakin da Yesu ya yi, sai suka fara cewa, “Lalle, wannan shi ne Annabin nan mai zuwa duniya.”
15 Chale Jesu ha lemuha kuti chivavali kusaka kukeza ni kumukwata che nkani kuti vamupange mulena, cha zwengera yenke kuma Lundu.
Da Yesu ya gane suna shirin su ɗauke shi ƙarfi da yaji su naɗa shi sarki, sai ya sāke komawa kan dutsen shi kaɗai.
16 Hachiyiza kuva chitengu, va lutwana vakwe chiva shetumukera kwi wate.
Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara zuwa tafki,
17 Chive chira muchikepe, mi vavali kuluta i wate kuya kwa Capenaume. Chikuvali kusiha cheyi nako, mi Jesu kena aveni kuka vola kale kuvali.
inda suka shiga jirgin ruwa suka tasar wa haye tafkin zuwa Kafarnahum. A lokacin kuwa duhu ya yi, Yesu kuma bai riga ya zo wurinsu ba tukuna.
18 Imi i huho likolete livali kuhunga, mi iwate chili vali kutangite kulwa.
Iska mai ƙarfi kuwa tana bugowa, ruwaye kuma suka fara hauka.
19 Hachi va zuhite chiuvaka chilikana makumi overe ni minwe ye yaza lyoke kamba makumi o tatwe muvule, chiva vona Jesu nakaya vuyenda he wulu lya wate ni kezite kumbali ni chikepe, mi vavali kutiyite.
Bayan sun yi tuƙi wajen mil uku ko uku da rabi, sai suka ga Yesu ya kusato jirgin ruwan, yana takawa a kan ruwan; sai suka tsorata.
20 Kono chati kuvali, “Njeme! Kanji mutiyi.”
Amma ya ce musu, “Ni ne; kada ku ji tsoro.”
21 Linu vavali kukusaka kumu longa muchi sepe, mi yahaho chisepe chicha kasika he rizo havavali kukaya.
Sa’an nan suka yarda suka karɓe shi a cikin jirgin ruwan, nan da nan kuwa jirgin ya kai gaɓar da za su.
22 Izuva lichilira, chinavungi chivali kuzimene kwishirya lye wate chiva vona kuti kena kuvena chimwi chikepe mbwita fera china choke, ni kuti Jesu kena ave chili mwateni ni varutwana vakwe kono kuti varutwana vakwe chivavali kuyendete vovona.
Kashegari taron da suka tsaya a wancan ƙetaren tafkin suka lura cewa jirgin ruwa ɗaya ne yake a can dā ma, kuma sun lura cewa Yesu bai shiga ciki tare da almajiransa ba, gama sun tashi su kaɗai.
23 Niha kuva vulyo, kuvena amwi mato avali kukazwa kwa Tiberiasi hafuhi ni chivaka aho hava liri vuroto uvo Simwine hava litumeri.
Sai ga waɗansu jiragen ruwa daga Tibariya suka iso kusa da wurin da mutanen suka ci burodi bayan Ubangiji ya yi godiya.
24 Linu china vungi hachi lemuha kuti nangati Jesu kamba varutwana vakwe kena vavali kusikwina, cwale avo vene chiva chira mumato ni kuyenda kwa Capenaume kuka ngana Jesu.
Da taron suka lura cewa Yesu da almajiransa ba sa can, sai suka shiga jiragen ruwa suka tafi Kafarnahum neman Yesu.
25 Hachiva manite kumuwana kweyina imwi imbali ye wate, chiva cho kwali, “Rabbi, wakeza liri kunu?”
Da suka same shi a wancan ƙetaren tafkin, sai suka tambaye shi suka ce, “Rabbi, yaushe ka kai nan?”
26 Jesu chave tava, ni kucho, “cho vuniti, niti, muni ngana, isiñi kuti muvavoni imakazo, kono ivaka lyokuti muvali vuroto vumwi bwe nkonko mi muve kuti.
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, kuna nemana ne ba don kun ga abubuwan banmamaki ba, sai dai domin kun ci burodi kun ƙoshi.
27 Kanji muverekeri zilyo inzo zisinyeha, kono muverekere zilyo zikala inako kutwala kuvahalo vusa mani uvo Mwana o Muntu bwasa mihe, kwe Ireeza Isi ava viki iswayo hali.” (aiōnios )
Kada ku yi aiki saboda abincin da yake lalacewa, sai dai saboda abinci mai dawwama har yă zuwa rai madawwami, wanda Ɗan Mutum zai ba ku. A kansa ne Allah Uba ya sa hatimin amincewarsa.” (aiōnios )
28 Cwale chivati kwali, “Chizi chi tuswanera ku panga, iri kuli tuwole kupanga misevezi ye Ireeza?”
Sai suka tambaye shi suka ce, “Me za mu yi don mu aikata ayyukan da Allah yake so?”
29 Jesu che tava ni kuta kuvali, “Uwu njo musevezi we Ireeza: kuti mu zumine ku yenke unzo yavaka tumi.”
Yesu ya amsa, “Aikin Allah shi ne, a gaskata da wanda ya aiko.”
30 Chwale chiva ta kwali, “Chechihi chisupo cwale choso pange, iri kuli tuvone ni kuku zumina? Chinzi choto pange?
Sai suka tambaye shi, “Wace abin banmamaki ce za ka yi don mu gani mu kuwa gaskata ka? Me za ka yi?
31 Veshetu vavali maana mwi halaupa, sina hakuñoletwe,'Avavahi inkonko izwa kwi wuulu kulya.”
Kakannin-kakanninmu sun ci Manna a hamada; kamar yadda yake a rubuce, ‘Ya ba su burodi daga sama su ci.’”
32 Linu Jesu chave tava, “Chovu niti, niti, kena ivali Mushe yava mihi inkonko kuzwa mwi wuulu, kono ivali Tayo yo miha inkonko ye niti izwa kwi wulu.
Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba Musa ne ya ba ku burodi daga sama ba, sai dai Ubana ne yake ba ku burodi na gaskiya daga sama.
33 Kakuti inkonko ye Ireeza je china chi zwa kwiwulu ni kukeza hansi ni kwiza kuha vuhalo kwi nkanda.”
Gama burodin Allah shi ne wanda yake saukowa daga sama, yana kuma ba wa duniya rai.”
34 Cwale chiva wamba kwali, “Nfumwetu, utuhe iyi inkonko inako yonse.”
Sai suka ce, “Ranka yă daɗe, daga yanzu ka dinga ba mu wannan burodi.”
35 Jesu cha wamba kuvali, “Jeme ni nkonko yo vuhalo; uzo yo keza kwangu kasane ka fwe inzala, mi uzo yo zumina mwangu kesane kafwe inyota.
Sa’an nan Yesu ya furta cewa, “Ni ne burodin rai. Wanda ya zo wurina ba zai taɓa jin yunwa ba, wanda kuma ya gaskata da ni ba zai taɓa jin ƙishirwa ba.
36 Kono ni vami wambiri chovu niti muvani voni, mi kamu zumini.
Amma kamar yadda na faɗa muku, kun gan ni duk da haka ba ku gaskata ba.
37 Yense uzo Tayo waniha mwa keze kwangu, mi yense yo keza kwangu chovuniti kaseni muzindire hanze.
Duk waɗanda Uba ya ba ni za su zo wurina, kuma duk wanda ya zo wurina ba zan kore shi ba ko kaɗan.
38 Kakuti niva kezi hansi kukazwa kwi wulu, isiñi kwiza kupanga itato yangu, kono chasaka iye uzo yavaka ni tumi.
Gama na sauko daga sama ba don in cika nufin kaina ba sai dai don in cika nufin shi wanda ya aiko ni.
39 Imi iyi nji tanto yakwe uzo yava kanitumi, kuti kanji ni zoverwa nangati yenke kwavo vonse vavanihi, kono kaniva vunse mwizuva lyama mani mani.
Nufin wanda ya aiko ni kuwa shi ne, kada in yar da ko ɗaya daga cikin duk waɗanda ya ba ni, sai dai in tashe su a rana ta ƙarshe.
40 Kakuli iyi nje tanto ya Tayo, kuti yense yo vona Mwana ni kuzumina mwali mwave ni vuhalo vusa mani mi kanimu vunse mwi zuva lya ma mani-mani. (aiōnios )
Gama nufin Ubana shi ne, duk wanda yake duban Ɗan, ya kuma gaskata shi zai sami rai madawwami, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.” (aiōnios )
41 Cwale majunda chivatanga kukumbola kuamana naye kakuti avati, “Njeme ni nkonko iyo yaka zwa kwi wulu.”
Da jin haka, Yahudawa suka fara gunaguni a kansa, domin ya ce, “Ni ne burodin da ya sauka daga sama.”
42 Chiva wamba, “Uzu kanjiyena Jesu mwana wa Josefa, uzo insi ni nyina tuve zi? Kwiza vule hape hanu kuti awambe, 'Nakazwa kwi wulu '?”
Suka ce, “Kai, wannan ba Yesu ba ne, ɗan Yusuf, wanda mahaifinsa da mahaifiyarsa duk mun san su? Yaya yanzu zai ce, ‘Na sauko daga sama?’”
43 Jesu che tava ni kuvata, “Musiye kukumbola mukati kenu.
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ku daina gunaguni a junanku.
44 Kakwina zumwi yo wola kukeza kwangu mbwita Tayo yava kanitumi hamu chuza, mi kani muvunse mwi zuva lyama mani-mani.
Ba mai iya zuwa wurina, sai dai in Uban da ya aiko ni ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.
45 Ku ñoletwe muma porofita, 'Yense karutiwe nji Ireeza. 'Yense yava zuwi ni kulituta kwa Tayo ukeza kwangu.
A rubuce yake a cikin Annabawa cewa, ‘Allah zai koyar da dukansu.’Duk wanda ya saurari Uba, ya kuma koyi daga wurinsa, zai zo wurina.
46 Kena kuti vonse vava voni Tayo, mbwita fera iye yokazwa kwe Ireeza- ava voni Tayo.
Ba wanda ya taɓa ganin Uban, sai shi wanda ya zo daga Allah; shi ne kaɗai ya taɓa ganin Uban.
47 Chovu niti, niti, iye yo zumina wina vahalo vusa mani. (aiōnios )
Gaskiya nake gaya muku, wanda ya gaskata yana da rai madawwami. (aiōnios )
48 Jeme ni nkonko yo vuhalo.
Ni ne burodin rai.
49 Veshenu vavali maana mwi halaupa, mi vava mani kufwa.
Kakannin-kakanninku sun ci Manna a hamada, duk da haka suka mutu.
50 Iyi nje nkonko ikeza hansi kukazwa kwi wulu, iri kuli muntu awole kulya yimwi kuili ni kusa fwa.
Amma ga burodin da ya sauko daga sama, wanda mutum zai iya ci, ba zai kuma mutu ba.
51 Jeme ni nkonko i hala iyo ikazwa kwi wulu. Haiva zumwi ulya kuili iyi nkonko, mwa hale kuya kuire. Inkonko iyo yete nihe inyama wangu kuvu halo vwe kanda.” (aiōn )
Ni ne burodin rai mai saukowa daga sama. Duk wanda ya ci wannan burodi, zai rayu har abada. Wannan burodin shi ne jikina, da zan bayar don duniya ta sami rai.” (aiōn )
52 Majunda chiva venga mukati kavo vene niku tanga kukanana, nivati, Kuwoleka vule kuti uzu mukwame atuhe inyama wakwe kuti tulye?'
Sai Yahudawa suka fara gardama mai tsanani a junansu suna cewa, “Yaya wannan mutum zai ba mu naman jikinsa mu ci?”
53 Cwale Jesu cha wamba kuvali, “Chovu niti, niti, kwanda yo kuti mulye inyama o Mwana o Muntu ni kunwa malaha akwe, kete muve ni vuhalo mwenu.
Sai Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, sai kun ci naman jikin Ɗan Mutum kuka kuma sha jininsa, ba za ku kasance da rai a cikinku ba.
54 Yense yolya inyama wangu ni kunwa malaha angu wina vuhalo vusa mani, mi kani muvuse mwizuvalya mamanikizo. (aiōnios )
Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana da rai madawwami. Ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe. (aiōnios )
55 Kakuti inyama yangu chilyo che niti, mi malaha angu chinwiwa che niti.
Gama naman jikina abinci ne na gaskiya jinina kuma abin sha ne na gaskiya.
56 Iye yo lya inyama wangu ni kunwa malaha angu ushala mwangu, ni me mwali.
Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana cikina, ni kuma ina cikinsa.
57 Sina Tayo yo hala havaka ni tumi, mi sina hani hala ivaka lya Tayo, cwale iye yonilya, mwahale naye ivaka lyangu.
Kamar dai yadda Uba mai rai ya aiko ni, ina kuma rayuwa ta saboda shi, haka ma wanda yake ni ne abincinsa zai rayu saboda ni.
58 Iyi nje nkonko ina yakeza hansi kukazwa kwi wulu, isiñi uvu veshenu vavali ni kufwa. Iye yo lya iyi nkonko mwahale kuya kuire.” (aiōn )
Wannan shi ne burodin da ya sauko daga sama. Kakannin-kakanninku sun ci Manna suka kuma mutu, amma duk wanda yake cin wannan burodi zai rayu har abada.” (aiōn )
59 Kono Jesu avali kuwamba inzi zintu mwi sinangonge na kwete kuruta mwa Capenaume.
Ya faɗi wannan ne lokacin da yake koyarwa a cikin majami’a a Kafarnahum.
60 Cwale vungi vwava rutwana vakwe vava zuwi izi chiva ti, “Iyi ituto ikavo ahulu; jeni yo wola kuitambula?”
Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, “Wannan koyarwa tana da wuya. Wa zai iya yarda da ita?”
61 Jesu, kakuli avali kwizi mwali kuti varutwana vakwe vavali kukumbola heyi dava, chati kuvali, “Kana ichi chimi nyeza?
Da yake ya san almajiransa suna gunaguni game da wannan, sai Yesu ya ce musu, “Wannan ya ɓata muku rai ne?
62 Cwale mukuve vule aho hasane kamuvone Mwana o Mutu nakambama kuta uko kwavali kwina sapilio?
Me za ku ce ke nan, in kuka gan Ɗan Mutum yana hawa zuwa inda yake dā!
63 Luhuho luha vuhalo; inyama kakwina chi ivozekeza. Mazwi awo ani vawambi kwenu nga luhuho, mi go vuhalo.
Ruhu ne yake ba da rai; jikin kam, ba ya amfana kome. Kalmomin da na faɗa muku, Ruhu ne, da kuma rai.
64 Imi kwina vamwi kwenu avo vasa zumini.”Kakuti Jesu avali kwinzi kuzwa kuma tangiro kuti mbani avo vate ni vakangwe kuzumina mi njeni uzo yate na muveteke.
Duk da haka akwai waɗansunku da ba su gaskata ba.” Gama Yesu ya sani tun farko, waɗanda ba su gaskata ba, da kuma wanda zai bashe shi.
65 Cha wamba, “I vaka lyezi kuti na miwamba kwenu kuti kakwina zumwi yo wola kukeza kwangu mbwita haiva wa zumininwa kwa Tayo.”
Ya ci gaba da cewa, “Shi ya sa na faɗa muku cewa ba mai iya zuwa wurina, sai dai Uba ya yardar masa.”
66 Kevaka lyezi, vungi bwa varutwana chiva vola kumusiya mi kena vavazwiri havusu ni kumwi chilira.
Daga wannan lokaci da yawa daga cikin almajiransa suka ja da baya, suka daina bin sa.
67 Linu Jesu cha wamba kuvana ikumi ni tovere, “Inwe nanwe kamusaki kuyenda nanwe, musaka?”
Sai Yesu ya tambayi Sha Biyun, “Ku ma za ku tafi ne?”
68 Simoni Pitorosi chamwi tava, “Simwine, njikwani kwete tuyende? Wina manzwi ovuhalo vusa mani, (aiōnios )
Sai Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji wajen wa za mu tafi? Kai ne da kalmomin rai madawwami. (aiōnios )
69 mi tuva zumini ni kwiza kwiziva kuti jewe yo Chena yenke we Ireeza.”
Mun gaskata mun kuma san cewa kai ne Mai Tsarkin nan na Allah.”
70 Jesu cha wamba kuvali, “Kena kuti ni vamiketi, vena ikumi ni minwe yovere, imi zumwi kwenu ji diavulusi?”
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ba ni na zaɓe ku Sha Biyu ba? Amma ɗayanku Iblis ne!”
71 Hanu avali kuwamba kuama ni Judasi mwana wa Simoni Isikariyoti, kakuti ivali iye, omumwina kuvena ikumi ni tovere, kakuti ivali njiyena, uzo yatane veteke Jesu.
(Yana nufin Yahuda, ɗan Siman Iskariyot, wanda, ko da yake ɗaya ne cikin Sha Biyun, zai bashe shi daga baya.)