< 시편 73 >
1 아삽의 시 하나님이 참으로 이스라엘 중 마음이 정결한 자에게 선을 행하시나
Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
2 나는 거의 실족할뻔 하였고 내 걸음이 미끄러질뻔 하였으니
Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
3 이는 내가 악인의 형통함을 보고 오만한 자를 질시하였음이로다
Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
4 저희는 죽는 때에도 고통이 없고 그 힘이 건강하며
Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
5 타인과 같은 고난이 없고 타인과 같은 재앙도 없나니
Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
6 그러므로 교만이 저희 목걸이요 강포가 저희의 입는 옷이며
Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
7 살찜으로 저희 눈이 솟아나며 저희 소득은 마음의 소원보다 지나며
Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
8 저희는 능욕하며 악하게 압제하여 말하며 거만히 말하며
Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
9 저희 입은 하늘에 두고 저희 혀는 땅에 두루 다니도다
Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
10 그러므로 그 백성이 이리로 돌아와서 잔에 가득한 물을 다 마시며
Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
11 말하기를 하나님이 어찌 알랴 지극히 높은 자에게 지식이 있으랴 하도다
Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
12 볼지어다 이들은 악인이라 항상 평안하고 재물은 더 하도다
Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
13 내가 내 마음을 정히 하며 내 손을 씻어 무죄하다 한 것이 실로 헛되도다
Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
14 나는 종일 재앙을 당하며 아침마다 징책을 보았도다
Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
15 내가 만일 스스로 이르기를 내가 이렇게 말하리라 하였더면 주의 아들들의 시대를 대하여 궤휼을 행하였으리이다
Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
16 내가 어찌면 이를 알까 하여 생각한즉 내게 심히 곤란하더니
Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
17 하나님의 성소에 들어갈 때에야 저희 결국을 내가 깨달았나이다
sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
18 주께서 참으로 저희를 미끄러운 곳에 두시며 파멸에 던지시니
Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
19 저희가 어찌 그리 졸지에 황폐되었는가 놀람으로 전멸하였나이다
Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
20 주여 사람이 깬 후에는 꿈을 무시함 같이 주께서 깨신 후에 저희 형상을 멸시하시리이다
Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
21 내 마음이 산란하며 내 심장이 찔렸나이다
Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
22 내가 이같이 우매 무지하니 주의 앞에 짐승이오나
na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
23 내가 항상 주와 함께하니 주께서 내 오른손을 붙드셨나이다
Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
24 주의 교훈으로 나를 인도하시고 후에는 영광으로 나를 영접하시리니
Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
25 하늘에서는 주 외에 누가 내게 있으리요 땅에서는 주 밖에 나의 사모할 자 없나이다
Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
26 내 육체와 마음은 쇠잔하나 하나님은 내 마음의 반석이시요 영원한 분깃이시라
Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
27 대저 주를 멀리하는 자는 망하리니 음녀 같이 주를 떠난 자를 주께서 다 멸하셨나이다
Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
28 하나님께 가까이 함이 내게 복이라 내가 주 여호와를 나의 피난처로 삼아 주의 모든 행사를 전파하리이다
Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.