< 시편 55 >
1 (다윗의 마스길. 영장으로 현악에 맞춘 노래) 하나님이여, 내 기도에 귀를 기울이시고 내가 간구할 때에 숨지 마소서
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
2 내게 굽히사 응답하소서! 내가 근심으로 편치 못하여 탄식하오니
ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
3 이는 원수의 소리와 악인의 압제의 연고라 저희가 죄악으로 내게 더하며 노하여 나를 핍박하나이다
hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
4 내 마음이 내 속에서 심히 아파하며 사망의 위험이 내게 미쳤도다
Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
5 두려움과 떨림이 내게 이르고 황공함이 나를 덮었도다
Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
6 나의 말이 내가 비둘기 같이 날개가 있으면 날아가서 편히 쉬리로다
Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
7 내가 멀리 날아가서 광야에 거하리로다 (셀라)
da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
8 내가 피난처에 속히 가서 폭풍과 광풍을 피하리라 하였도다
da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
9 내가 성내에서 강포와 분쟁을 보았사오니 주여, 저희를 멸하소서 저희 혀를 나누소서
Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
10 저희가 주야로 성벽 위에 두루 다니니 성중에는 죄악과 잔해함이 있으며
Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
11 악독이 그 중에 있고 압박과 궤사가 그 거리를 떠나지 않도다
Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
12 나를 책망한 자가 원수가 아니라 원수일진대 내가 참았으리라 나를 대하여 자기를 높이는 자가 나를 미워하는 자가 아니라 미워하는 자일진대 내가 그를 피하여 숨었으리라
Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
13 그가 곧 너로다 나의 동류, 나의 동무요 나의 가까운 친우로다
Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
14 우리가 같이 재미롭게 의논하며 무리와 함께 하여 하나님의 집안에서 다녔도다
wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
15 사망이 홀연히 저희에게 임하며 산 채로 음부에 내려갈지어다 이는 악독이 저희 거처에 있고 저희 가운데 있음이로다 (Sheol )
Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol )
16 나는 하나님께 부르짖으리니 여호와께서 나를 구원하시리로다
Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
17 저녁과 아침과 정오에 내가 근심하여 탄식하리니 여호와께서 내 소리를 들으시리로다
Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
18 나를 대적하는 자 많더니 나를 치는 전쟁에서 저가 내 생명을 구속하사 평안하게 하셨도다
Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
19 태고부터 계신 하나님이 들으시고 (셀라) 변치 아니하며 하나님을 경외치 아니하는 자에게 보응하시리로다
Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
20 저는 손을 들어 자기와 화목한 자를 치고 그 언약을 배반하였도다
Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
21 그 입은 우유기름보다 미끄러워도 그 마음은 전쟁이요 그 말은 기름보다 유하여도 실상은 뽑힌 칼이로다
Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
22 네 짐을 여호와께 맡겨 버리라 너를 붙드시고 의인의 요동함을 영영히 허락지 아니하시리로다
Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
23 하나님이여, 주께서 저희로 파멸의 웅덩이에 빠지게 하시리이다 피를 흘리게 하며 속이는 자들은 저희 날의 반도 살지 못할 것이나 나는 주를 의지하리이다
Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.