< 시편 3 >

1 (다윗이 그 아들 압살롬을 피할 때에 지은 시) 여호와여, 나의 대적이 어찌 그리 많은지요 일어나 나를 치는 자가 많소이다
Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
2 많은 사람이 있어 나를 가리켜 말하기를 저는 하나님께 도움을 얻지 못한다 하나이다 (셀라)
Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
3 여호와여, 주는 나의 방패시요 나의 영광이시요 나의 머리를 드시는 자니이다
Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
4 내가 나의 목소리로 여호와께 부르짖으니 그 성산에서 응답하시는도다 (셀라)
Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
5 내가 누워 자고 깨었으니 여호와께서 나를 붙드심이로다 내가 누워 자고 깨었으니 여호와께서 나를 붙드심이로다
Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
6 천만인이 나를 둘러치려 하여도 나는 두려워 아니하리이다
Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
7 여호와여, 일어나소서 나의 하나님이여, 나를 구원하소서 주께서 나의 모든 원수의 뺨을 치시며 악인의 이를 꺽으셨나이다
Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
8 구원은 여호와께 있사오니 주의 복을 주의 백성에게 내리소서 (셀라)
Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)

< 시편 3 >