< 시편 118 >

1 여호와께 감사하라! 저는 선하시며 그 인자하심이 영원함이로다
Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 이제 이스라엘은 말하기를 그 인자하심이 영원하다 할지로다
Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
3 이제 아론의 집은 말하기를 그 인자하심이 영원하다 할지로다
Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
4 이제 여호와를 경외하는 자는 말하기를 그 인자하심이 영원하다 할지로다
Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
5 내가 고통 중에 여호와께 부르짖었더니 여호와께서 답하시고 나를 광활한 곳에 세우셨도다
Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
6 여호와는 내 편이시라 내게 두려움이 없나니 내게 어찌할꼬
Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
7 여호와께서 내 편이 되사 나를 돕는 자 중에 계시니 그러므로 나를 미워하는 자에게 보응하시는 것을 내가 보리로다
Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
8 여호와께 피함이 사람을 신뢰함보다 나으며
Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
9 여호와께 피함이 방백들을 신뢰함보다 낫도다
Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.

< 시편 118 >