< 시편 105 >

1 여호와께 감사하며 그 이름을 불러 아뢰며 그 행사를 만민 중에 알게 할지어다
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
2 그에게 노래하며 그를 찬양하며 그의 모든 기사를 말할지어다
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
3 그 성호를 자랑하라 무릇 여호와를 구하는 자는 마음이 즐거울지로다
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
4 여호와와 그 능력을 구할지어다 그 얼굴을 항상 구할지어다
Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
5 그 종 아브라함의 후손 곧 택하신 야곱의 자손 너희는 그의 행하신 기사와 그 이적과 그 입의 판단을 기억할지어다
Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
6 (5절과 같음)
Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
7 그는 여호와 우리 하나님이시라 그의 판단이 온 땅에 있도다
Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
8 그는 그 언약 곧 천대에 명하신 말씀을 영원히 기억하셨으니
Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
9 이것은 아브라함에게 하신 언약이며 이삭에게 하신 맹세며
alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
10 야곱에게 세우신 율례 곧 이스라엘에게 하신 영영한 언약이라
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
11 이르시기를 내가 가나안 땅을 네게 주어 너희 기업의 지경이 되게 하리라 하셨도다
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
12 때에 저희 인수가 적어 매우 영성하며 그 땅에 객이 되어
Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
13 이 족속에게서 저 족속에게로, 이 나라에서 다른 민족에게로 유리하였도다
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
14 사람이 그들을 해하기를 용납지 아니하시고 그들의 연고로 열왕을 꾸짖어
Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
15 이르시기를 나의 기름 부은 자를 만지지 말며 나의 선지자를 상하지 말라 하셨도다
“Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
16 그가 또 기근을 불러 그 땅에 임하게 하여 그 의뢰하는 양식을 다 끊으셨도다
Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
17 한 사람을 앞서 보내셨음이여 요셉이 종으로 팔렸도다
ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
18 그 발이 착고에 상하며 그 몸이 쇠사슬에 매였으니
Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
19 곧 여호와의 말씀이 응할 때까지라 그 말씀이 저를 단련하였도다
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
20 왕이 사람을 보내어 저를 방석함이여 열방의 통치자가 저로 자유케 하였도다
Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
21 저로 그 집의 주관자를 삼아 그 모든 소유를 관리케 하고
Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
22 임의로 백관을 제어하며 지혜로 장로들을 교훈하게 하였도다
don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
23 이에 이스라엘이 애굽에 들어감이여 야곱이 함 땅에 객이 되었도다
Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
24 여호와께서 그 백성을 크게 번성케 하사 그들의 대적보다 강하게 하셨으며
Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
25 또 저희 마음을 변하여 그 백성을 미워하게 하시며 그 종들에게 교활히 행하게 하셨도다
waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
26 또 그 종 모세와 그 택하신 아론을 보내시니
Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
27 저희가 그 백성 중에 여호와의 표징을 보이고 함 땅에서 기사를 행하였도다
Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
28 여호와께서 흑암을 보내사 어둡게 하시니 그 말씀을 어기지 아니하였도다
Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
29 저희 물을 변하여 피가 되게 하사 저희 물고기를 죽이셨도다
Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
30 그 땅에 개구리가 번성하여 왕의 궁실에도 있었도다
Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
31 여호와께서 말씀 하신즉 파리떼가 오며 저희 사경에 이가 생겼도다
Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
32 비 대신 우박을 내리시며 저희 땅에 화염을 내리셨도다
Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
33 저희 포도나무와 무화과나무를 치시며 저희 사경의 나무를 찍으셨도다
ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
34 여호와께서 말씀하신즉 황충과 무수한 메뚜기가 이르러
Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
35 저희 땅에 모든 채소를 먹으며 그 밭에 열매를 먹었도다
suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
36 여호와께서 또 저희 땅의 모든 장자를 치시니 곧 저희 모든 기력의 시작이로다
Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
37 그들을 인도하여 은금을 가지고 나오게 하시니 그 지파 중에 약한 자가 하나도 없었도다
Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
38 그들의 떠날 때에 애굽이 기뻐하였으니 저희가 그들을 두려워함이로다
Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
39 여호와께서 구름을 펴사 덮개를 삼으시고 밤에 불로 밝히셨으며
Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
40 그들이 구한즉 메추라기로 오게 하시며 또 하늘 양식으로 그들을 만족케 하셨도다
Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
41 반석을 가르신즉 물이 흘러나서 마른 땅에 강 같이 흘렀으니
Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
42 이는 그 거룩한 말씀과 그 종 아브라함을 기억하셨음이로다
Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
43 그 백성으로 즐거이 나오게 하시며 그 택한 자로 노래하며 나오게 하시고
Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
44 열방의 땅을 저희에게 주시며 민족들의 수고한 것을 소유로 취하게 하셨으니
ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
45 이는 저희로 그 율례를 지키며 그 법을 좇게 하려 하심이로다 할렐루야!
don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.

< 시편 105 >