< 시편 102 >

1 (곤고한 자가 마음이 상하여 그 근심을 여호와 앞에 토하는 기도) 여호와여, 내 기도를 들으시고 나의 부르짖음을 주께 상달케 하소서
Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
2 나의 괴로운 날에 주의 얼굴을 내게 숨기지 마소서 주의 귀를 기울이사 내가 부르짖는 날에 속히 내게 응답하소서
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
3 대저 내 날이 연기 같이 소멸하며 내 뼈가 냉과리 같이 탔나이다
Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
4 내가 음식 먹기도 잊었음으로 내 마음이 풀 같이 쇠잔하였사오며
Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
5 나의 탄식 소리를 인하여 나의 살이 뼈에 붙었나이다
Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
6 나는 광야의 당아새 같고 황폐한 곳의 부엉이 같이 되었사오며
Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
7 내가 밤을 새우니 지붕 위에 외로운 참새 같으니이다
Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
8 내 원수들이 종일 나를 훼방하며 나를 대하여 미칠듯이 날치는 자들이 나를 가리켜 맹세하나이다
Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
9 나는 재를 양식 같이 먹으며 나의 마심에는 눈물을 섞었사오니
Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
10 이는 주의 분과 노를 인함이라 주께서 나를 드셨다가 던지셨나이다
saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
11 내 날이 기울어지는 그림자 같고 내가 풀의 쇠잔함 같으니이다
Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
12 여호와여, 주는 영원히 계시고 주의 기념 명칭은 대대에 이르리이다
Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
13 주께서 일어나사 시온을 긍휼히 여기시리니 지금은 그를 긍휼히 여기실 때라 정한 기한이 옴이니이다
Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
14 주의 종들이 시온의 돌들을 즐거워하며 그 티끌도 연휼히 여기나이다
Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
15 이에 열방이 여호와의 이름을 경외하며 세계 열왕이 주의 영광을 경외하리니
Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
16 대저 여호와께서 시온을 건설하시고 그 영광 중에 나타나셨음이라
Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
17 여호와께서 빈궁한 자의 기도를 돌아보시며 저희 기도를 멸시치 아니하셨도다
Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
18 이 일이 장래 세대를 위하여 기록되리니 창조함을 받을 백성이 여호와를 찬송하리로다
Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
19 여호와께서 그 높은 성소에서 하감하시며 하늘에서 땅을 감찰하셨으니
“Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
20 이는 갇힌자의 탄식을 들으시며 죽이기로 정한 자를 해방하사
don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
21 여호와의 이름을 시온에서 그 영예를 예루살렘에서 선포케 하려 하심이라
Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
22 때에 민족들과 나라들이 모여 여호와를 섬기리로다
sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
23 저가 내 힘을 중도에 쇠약케 하시며 내 날을 단촉케 하셨도다
Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
24 나의 말이 나의 하나님이여, 나의 중년에 나를 데려가지 마옵소서 주의 연대는 대대에 무궁하니이다
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
25 주께서 옛적에 땅의 기초를 두셨사오며 하늘도 주의 손으로 지으신 바니이다
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
26 천지는 없어지려니와 주는 영존하시겠고 그것들은 다 옷 같이 낡으리니 의복같이 바꾸시면 바뀌려니와
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
27 주는 여상하시고 주의 년대는 무궁하리이다
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
28 주의 종들의 자손이 항상 있고 그 후손이 주의 앞에 굳게 서리이다 하였도다
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”

< 시편 102 >