< 요한복음 10 >

1 내가 진실로 진실로 너희에게 이르노니 양의 우리에 문으로 들어가지 아니하고 다른데로 넘어가는 자는 절도며 강도요
“Hakika, Hakika, ina ce maku, wanda bai shiga ta kofa zuwa garken tumaki ba, amma ya haura ta wata hanya, wannan mutum barawo ne da dan fashi.
2 문으로 들어가는 이가 양의 목자라
Wanda ya shiga ta kofa shine makiyayin tumakin.
3 문지기는 그를 위하여 문을 열고 양은 그의 음성을 듣나니 그가 자기 양의 이름을 각각 불러 인도하여 내느니라
Mai gadin kofar zai bude masa. Tumakin suna jin muryarsa, ya na kuma kiran tumakinsa da sunayensu, ya kuma kai su waje.
4 자기 양을 다 내어 놓은 후에 앞서 가면 양들이 그의 음성을 아는고로 따라 오되
Bayanda ya kawo su duka a waje, yana tafiya a gabansu, sai tumakin su bi shi, domin sun san muryarsa.
5 타인의 음성은 알지 못하는고로 타인을 따르지 아니하고 도리어 도망하느니라'
Ba za su bi bako ba amma sai dai su guje shi, domin basu san muryar baki ba.”
6 예수께서 이 비유로 저희에게 말씀하셨으나 저희는 그 하신 말씀이 무엇인지 알지 못하니라
Yesu ya yi masu magana da wannan misali, amma basu gane wadannan abubuwa da yake gaya masu ba.
7 그러므로 예수께서 다시 이르시되 `내가 진실로 진실로 너희에게 말하노니 나는 양의 문이라
Sai Yesu ya ce masu kuma, “Hakika, Hakika, Ina ce maku, Ni ne kofar tumaki.
8 나보다 먼저 온 자는 다 절도요 강도니 양들이 듣지 아니하였느니라
Dukan wadanda suka zo kamin ni barayi ne da yan fashi, amma tumakin ba su ji su ba.
9 내가 문이니 누구든지 나로 말미암아 들어가면 구원을 얻고 또는 들어가며 나오며 꼴을 얻으리라
Ni ne kofa, In kowa ya shiga ta wurina, zai sami ceto, zai shiga ya fita ya kuma sami wurin kiwo.
10 도적이 오는 것은 도적질하고 죽이고 멸망시키려는 것뿐이요 내가 온 것은 양으로 생명을 얻게 하고 더 풍성히 얻게 하려는 것이라
Barawo ba ya zuwa sai don ya yi sata, ya kashe, ya kuma hallakar. Na zo ne domin su sami rai su kuma same shi a yalwace.
11 나는 선한 목자라! 선한 목자는 양들을 위하여 목숨을 버리거니와
Ni ne makiyayi mai kyau. Makiyayi mai kyau yana bada ransa domin tumakinsa.
12 삯군은 목자도 아니요 양도 제 양이 아니라 이리가 오는 것을 보면 양을 버리고 달아나나니 이리가 양을 늑탈하고 또 헤치느니라
Wanda yake dan sako kuma, ba makiyayi ba, wanda ba shine mai tumakin ba, in ya ga kyarkeci na zuwa sai ya saki tumakin ya gudu. Sai kyarkecin ya dauke su ya kuma warwatsa su.
13 달아나는 것은 저가 삯군인 까닭에 양을 돌아보지 아니함이나
Ya gudu domin shi mai aikin kudi ne kuma bai damu da tumakin ba.
14 나는 선한 목자라! 내가 내 양을 알고 양도 나를 아는 것이
Nine makiyayi mai kyau, na kuma san nawa, nawa kuma sun san ni.
15 아버지께서 나를 아시고 내가 아버지를 아는 것 같으니 나는 양을 위하여 목숨을 버리노라
Uban ya san ni, ni ma na san Uban, na kuma bada raina domin tumakin.
16 또 이 우리에 들지 아니한 다른 양들이 내게 있어 내가 인도하여야 할 터이니 저희도 내 음성을 듣고 한 무리가 되어 한 목자에게 있으리라
Ina da wadansu tumaki wadanda ba na wannan garken ba. Wadannan, kuma, dole in kawo su, su ma za su ji muryata saboda za su zama garke daya da makiyayi daya.
17 아버지께서 나를 사랑하시는 것은 내가 다시 목숨을 얻기 위하여 목숨을 버림이라
Domin wannan ne Uban yake kauna ta: Na bada raina domin in same shi kuma.
18 이를 내게서 빼앗는 자가 있는 것이 아니라 내가 스스로 버리노라 나는 버릴 권세도 있고 다시 얻을 권세도 있으니 이 계명은 내 아버지에게서 받았노라' 하시니라
Babu wanda zai dauke shi daga wurina, amma ina bayar da shi da kaina. Ina da ikon bada shi, ina da iko in dauke shi kuma. Na karbi wannan umarnin daga wurin Ubana.”
19 이 말씀을 인하여 유대인 중에 다시 분쟁이 일어나니
Tsattsaguwa ta sake tashi tsakanin Yahudawa domin wadannan kalmomin.
20 그 중에 많은 사람이 말하되 `저가 귀신 들려 미쳤거늘 어찌하여 그 말을 듣느냐?' 하며
Dayawa a cikinsu suka ce, yana da aljani, kuma mahaukaci ne. Don me ku ke sauraronsa?”
21 혹은 말하되 `이 말은 귀신들린 자의 말이 아니라 귀신이 소경의 눈을 뜨게 할 수 있느냐?' 하더라
Wadansu suka ce, wadannan ba kalmomin wanda yake da aljani ba ne. Ko mai aljani zai iya bude idanun makaho?”
22 예루살렘에 수전절이 이르니 때는 겨울이라
Sai lokacin idin Tsarkakewa a Urushalima ya zo.
23 예수께서 성전 안 솔로몬 행각에서 다니시니
A lokacin damuna ne, Yesu kuwa yana tafiya a shirayi cikin haikalin Sulaimanu.
24 유대인들이 에워싸고 가로되 `당신이 언제까지나 우리 마음을 의혹케 하려나이까? 그리스도여든 밝히 말하시오' 하니
Sai Yahudawa suka zagaye shi suka ce masa, “Har yaushe ne za ka bar mu cikin shakka? In kai ne Almasihun, ka gaya mana dalla-dalla.”
25 예수께서 대답하시되 `내가 너희에게 말하였으되 믿지 아니하는도다 내가 내 아버지의 이름으로 행하는 일들이 나를 증거하는 것이어늘
Yesu ya ce masu, “Na gaya maku, amma baku gaskata ba. Ayyukan da nake yi a cikin sunan Ubana, su ke yin shaida a kaina.
26 너희가 내 양이 아니므로 믿지 아니하는도다
Duk da haka baku gaskata ba domin ku ba tumakina ba ne.
27 내 양은 내 음성을 들으며 나는 저희를 알며 저희는 나를 따르느니라
Tumakina suna jin murya ta; Na san su, suna kuma bi na.
28 내가 저희에게 영생을 주노니 영원히 멸망치 아니할 터이요 또 저희를 내 손에서 빼앗을 자가 없느니라 (aiōn g165, aiōnios g166)
Ina ba su rai na har abada; ba za su taba mutuwa ba, babu wanda zai kwace su daga hannu na. (aiōn g165, aiōnios g166)
29 저희를 주신 내 아버지는 만유보다 크시매 아무도 아버지 손에서 빼앗을 수 없느니라!
Ubana, wanda ya bani su, ya fi kowa girma, kuma ba mai iya kwace su daga hannun Uban.
30 나와 아버지는 하나이니라' 하신대
Ni da Uban daya ne.”
31 유대인들이 다시 돌을 들어 치려 하거늘
Sai Yahudawa suka dauki duwatsu kuma domin su jajjefe shi.
32 예수께서 대답하시되 `내가 아버지께로 말미암아 여러 가지 선한 일을 너희에게 보였거늘 그 중에 어떤 일로 나를 돌로 치려 하느냐?'
Yesu ya amsa masu, “Na nuna maku kyawawan ayyuka masu yawa daga wurin Uban. Saboda wane daga cikin wadannan ayyukan kuke jefe ni?”
33 유대인들이 대답하되 `선한 일을 인하여 우리가 너를 돌로 치려는 것이 아니라 참람함을 인함이니 네가 사람이 되어 자칭 하나님이라 함이로라'
Sai Yahudawa suka amsa masa, “ba don wani aiki mai kyau muke son mu jefe ka ba, amma don sabo, domin kai, mutum ne, amma kana mayar da kanka Allah.”
34 예수께서 가라사대 `너희 율법에 기록한바 내가 너희를 신이라 하였노라 하지 아니하였느냐
Yesu ya amsa masu, “Ba a rubuce yake a shari'arku ba, 'Na ce, “ku alloli ne”'?”
35 성경은 폐하지 못하나니 하나님의 말씀을 받은 사람들을 신이라 하셨거든
In ya kira su alloli, su wadanda maganar Allah ta zo gare su (kuma ba za a iya karya nassi ba),
36 하물며 아버지께서 거룩하게 하사 세상에 보내신 자가 나는 하나님 아들이라 하는 것으로 너희가 어찌 참람하다 하느냐?
kuna gaya wa wanda Uban ya kebe ya kuma aiko cikin duniya, 'Kana sabo', domin Na ce, 'Ni dan Allah ne'?
37 만일 내가 내 아버지의 일을 행치 아니하거든 나를 믿지 말려니와
In ba na aikin Ubana, kada ku gaskata ni.
38 내가 행하거든 나를 믿지 아니할지라도 그 일은 믿으라! 그러면 너희가 아버지께서 내 안에 계시고 내가 아버지 안에 있음을 깨달아 알리라' 하신대
Amma, idan ina yin su, ko ba ku gaskata da ni ba, ku gaskata da ayyukan saboda ku sani, ku kuma gane cewa Uban yana ciki na, ni kuma ina cikin Uban.”
39 저희가 다시 예수를 잡고자 하였으나 그 손에서 벗어나 나가시니라
Suka sake kokarin kama shi, amma ya yi tafiyarsa, ya fita daga hannunsu.
40 다시 요단강 저편 요한이 처음으로 세례 주던 곳에 가사 거기 거하시니
Ya yi tafiyarsa kuma har gaba da kogin Urdun zuwa inda Yahaya ke yin baftisma ada, ya kuma zauna a wurin.
41 많은 사람이 왔다가 말하되 `요한은 아무 표적도 행치 아니하였으나 요한이 이 사람을 가리켜 말한 것은 참이라' 하더라
Mutane masu yawa suka zo wurinsa, suka ce,”Hakika Yahaya bai yi wasu alamu ba, amma dukan abubuwan da Yahaya ya ce game da wannan mutum gaskiya ne.”
42 그리하여 거기서 많은 사람이 예수를 믿으니라
Mutane dayawa suka bada gaskiya gare shi a wurin.

< 요한복음 10 >