< 욥기 8 >

1 수아 사람 빌닷이 대답하여 가로되
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 네가 어느 때까지 이런 말을 하겠으며 어느 때까지 네 입의 말이 광풍과 같겠는가
“Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
3 하나님이 어찌 심판을 굽게 하시겠으며 전능하신이가 어찌 공의를 굽게 하시겠는가
Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
4 네 자녀들이 주께 득죄하였으므로 주께서 그들을 그 죄에 붙이셨나니
Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
5 네가 만일 하나님을 부지런히 구하며 전능하신 이에게 빌고
Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
6 또 청결하고 정직하면 정녕 너를 돌아보시고 네 의로운 집으로 형통하게 하실 것이라
in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
7 네 시작은 미약하였으나 네 나중은 심히 창대하리라
Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
8 청컨대 너는 옛시대 사람에게 물으며 열조의 터득한 일을 배울지어다
“Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
9 (우리는 어제부터 있었을 뿐이라 지식이 망매하니 세상에 있는 날이 그림자와 같으니라)
gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
10 그들이 네게 가르쳐 이르지 아니하겠느냐 그 마음에서 나는 말을 발하지 아니하겠느냐
Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
11 왕골이 진펄이 아니고 나겠으며 갈대가 물 없이 자라겠느냐
Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
12 이런 것은 푸르러도 아직 벨 때 되기 전에 다른 풀보다 일찌기 마르느니라
Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
13 하나님을 잊어버리는 자의 길은 다 이와 같고 사곡한 자의 소망은 없어지리니
Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
14 그 믿는 것이 끊어지고 그 의지하는 것이 거미줄 같은즉
Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
15 그 집을 의지할지라도 집이 서지 못하고 굳게 잡아도 집이 보존 되지 못하리라
Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
16 식물이 일광을 받고 푸르러서 그 가지가 동산에 벋어가며
Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
17 그 뿌리가 돌 무더기에 서리어서 돌 가운데로 들어 갔을지라도
shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
18 그 곳에서 뽑히면 그 자리도 모르는 체하고 이르기를 내가 너를 보지 못하였다 하리니
Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
19 그 길의 희락은 이와 같고 그 후에 다른 것이 흙에서 나리라
Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
20 하나님은 순전한 사람을 버리지 아니하시고 악한 자를 붙들어 주지 아니하신즉
“Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
21 웃음으로 네 입에, 즐거운 소리로 네 입술에 채우시리니
Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
22 너를 미워하는 자는 부끄러움을 입을 것이라 악인의 장막은 없어지리라
Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”

< 욥기 8 >