< 욥기 36 >

1 엘리후가 말을 이어 가로되
Elihu ya ci gaba,
2 나를 잠간 용납하라 내가 네게 보이리니 이는 내가 하나님을 위하여 오히려 할 말이 있음이라
“Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
3 내가 먼 데서 지식을 취하고 나를 지으신 자에게 의를 돌려 보내리라
Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
4 진실로 내 말이 거짓이 아니라 지식이 구비한 자가 너와 함께 있느니라
Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
5 하나님은 전능하시나 아무도 멸시치 아니하시며 그 지능이 무궁하사
“Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
6 악인을 살려 두지 않으시며 고난 받는 자를 위하여 신원하시며
Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
7 그 눈을 의인에게서 돌이키지 아니하시고 그를 왕과 함께 영원히 위에 앉히사 존귀하게 하시며
Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
8 혹시 그들이 누설에 매이거나 환난의 줄에 얽혔으면
Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
9 그들의 소행과 허물을 보이사 그 교만한 행위를 알게 하시고
yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
10 그들의 귀를 열어 교훈을 듣게 하시며 명하여 죄악에서 돌아오게 하시나니
Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
11 만일 그들이 청종하여 섬기면 형통히 날을 보내며 즐거이 해를 지낼 것이요
In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
12 만일 그들이 청종치 아니하면 칼에 망하며 지식 없이 죽을 것이니라
Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
13 마음이 사곡한 자들은 분노를 쌓으며 하나님께 속박을 받을지라도 도우심을 구하지 아니하나니
“Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
14 그들은 젊어서 죽으며 그 생명이 남창과 함께 망하려니와
Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
15 하나님은 곤고한 자를 그 곤고할 즈음에 구원하시며 학대 당할 즈음에 그 귀를 여시나니
Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
16 그러므로 하나님이 너를 곤고함에서 이끌어 내사 좁지 않고 넓은곳으로 옮기려 하셨은즉 무릇 네 상에 차린 것은 살진 것이 되었으리라
“Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
17 이제는 악인의 받을 벌이 네게 가득하였고 심판과 공의가 너를 잡았나니
Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
18 너는 분격함을 인하여 징책을 대적하지 말라 대속함을 얻을 일이 큰즉 스스로 그릇되게 말지니라
Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
19 너의 부르짖음이나 너의 세력이 어찌 능히 너의 곤고한 가운데서 너로 유익하게 하겠느냐
Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
20 너는 밤 곧 인생이 자기 곳에서 제함을 받는 때를 사모하지 말것이니라
Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
21 삼가 악으로 치우치지 말라 네가 환난보다 이것을 택하였느니라
Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
22 하나님은 그 권능으로 큰 일을 행하시나니 누가 그 같이 교훈을 베풀겠느냐
“An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
23 누가 그를 위하여 그의 길을 정하였느냐 누가 말하기를 주께서 불의를 행하셨나이다 할 수 있으랴
Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
24 너는 하나님의 하신 일 찬송하기를 잊지 말지니라 인생이 그 일을 노래하였느니라
Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
25 그 일을 모든 사람이 우러러 보나니 먼데서도 보느니라
Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
26 하나님은 크시니 우리가 그를 알 수 없고 그 년수를 계산할 수 없느니라
Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
27 그가 물을 가늘게 이끌어 올리신즉 그것이 안개 되어 비를 이루고
“Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
28 그것이 공중에서 내려 사람 위에 쏟아지느니라
Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
29 구름의 폐임과 그의 장막의 울리는 소리를 누가 능히 깨달으랴
Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
30 그가 번개 빛으로 자기의 사면에 두르시며 바다 밑도 가리우시며
Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
31 이런 것들로 만민을 징벌하시며 이런 것들로 식물을 풍비히 주시느니라
Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
32 그는 번개 빛으로 그 두 손을 싸시고 그것을 명하사 푯대를 맞추게 하시나니
Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
33 그 울리는 소리가 풍우를 표시하고 육축에게까지 그 올라 오는 것을 표시하느니라
Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.

< 욥기 36 >