< 욥기 35 >

1 엘리후가 말을 이어 가로되
Sai Elihu ya ce,
2 네가 이것을 합리하게 여기느냐 네 생각에 네가 하나님보다 의롭다 하여
“Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
3 이르기를 유익이 무엇인고 범죄한 것보다 내게 이익이 무엇인고 하는구나
Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
4 내가 너와 및 너와 함께 있는 네 동무들에게 대답하리라
“Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
5 너는 하늘을 우러러 보라 네 위의 높은 궁창을 바라보라
Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
6 네가 범죄한들 하나님께 무슨 영향이 있겠으며 네 죄악이 관영한들 하나님께 무슨 관계가 있겠으며
In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
7 네가 의로운들 하나님께 무엇을 드리겠으며 그가 네 손에서 무엇을 받으시겠느냐
In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
8 네 악은 너와 같은 사람이나 해할 따름이요 네 의는 인생이나 유익하게 할 뿐이니라
Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
9 사람은 학대가 많으므로 부르짖으며 세력 있는 자의 팔에 눌리므로 도움을 부르짖으나
“Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
10 나를 지으신 하나님 곧 사람으로 밤중에 노래하게 하시며 우리를 교육하시기를 땅의 짐승에게 하심보다 더하게 하시며 우리에게 지혜 주시기를 공중의 새에게 주심보다 더하시는 이가 어디 계신가 말하는 자가 한 사람도 없구나
Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
11 상동
wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
12 그들이 악인의 교만을 인하여 거기서 부르짖으나 응락하는 자가 없음은
Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
13 헛된 부르짖음은 하나님이 결코 듣지 아니하시며 전능자가 돌아 보지 아니 하심이라
Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
14 하물며 말하기를 하나님은 뵈올 수 없고 일의 시비는 그 앞에 있으니 나는 그를 기다릴 뿐이라 하는 너랴
Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
15 하나님이 진노하심으로 벌을 주지 아니하셨고 횡포를 심히 살피지 아니하셨으므로
Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
16 이제 너 욥이 헛되이 입을 열어 지식 없는 말을 많이 하는구나
Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”

< 욥기 35 >