< Marko 3 >
1 Ni kabhele akajhingila mugati mu lisinagogi na m'ola jaajhele ni munu jhaapoozili kibhoko.
Wani lokaci, da ya sāke shiga majami’a, sai ga wani mutum mai shanyayyen hannu.
2 Baadhi jha bhanu bhankeseleleghe kwa bhuharibifu kulola Kama ibetakujobha ligono lya Sabato ili kwamba bhan'shtakiajhi.
Waɗansu daga cikin mutane suna neman dalilin zargin Yesu, sai suka zuba masa ido, su ga ko zai warkar da shi a ranar Asabbaci.
3 Yesu akan'jobhela munu jha apoozili kibhokho,” Jhinukayi na ujhemayi katikati jha bhumati obho.”
Yesu ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.”
4 Kisha akabhajobhela bhanu, “Je ni halali kubhomba khenu kinofu ligono lya Sabato au kubhomba ghaghabelili kuj'ha gha haki; kuokola maisha, au kukoma?” Lakini bhakabakila kinunu.
Sai Yesu ya tambaye su ya ce, “Me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci, a aikata alheri, ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a yi kisa?” Amma suka yi shiru.
5 Akabhalanga kwa ligoga, akajhaihuzunika kwa ndabha j'ha bhubomolaji bhwa mioyo ghyabhene na akan'jobhela munu jhola, “Nyosiajhi kibhokho Kya jhobhi”. Akabhunyoosya ni Yesu akamponesya kibhokho Kya muene.
Sai ya kalle su da fushi, don taurin zuciyarsu ya ɓata masa rai sosai. Sai ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.
6 Mafarisayo bhakalota kwibhala na mara bhakabhomba njama pamonga ni Maherode dhidi jha muene ili kun'koma.
Sai Farisiyawa suka fita, suka fara ƙulla shawara da mutanen Hiridus yadda za su kashe Yesu.
7 Kisha Yesu pamonga ni bhanafunzi bha muene, bhakalota kubahari, ni bhumati mbaha bhwa bhanu ghwabhakesisi kuh'omela Galilaya ni Bhuyahudi
Yesu da almajiransa suka janye zuwa tafkin, taro mai yawa kuwa daga Galili ya bi shi.
8 ni kuh'omela Yerusalemu ni kuh'omela Idumaya ni palongolo jha Yorodani hi jirani jha Tiro ni Sidoni, bhumati mbaha, bhobhup'eliki khila khenu Kya abhombekai, bhahidili kwa muene.
Mutane da yawa daga Yahudiya, da Urushalima, da Edom, da kuma yankunan da suke ƙetaren Urdun, da kewayen Taya, da Sidon suka zo wurinsa, don sun ji dukan abubuwan da yake yi.
9 Na abhajobhili bhanafunzi bha muene kuandala bhuatu bhudebe kwa ndabha jha bhumati ili kwamba bhasihidi kun'komanila.
Saboda taron, sai ya ce wa almajiransa su shirya masa ƙaramin jirgin ruwa, don kada mutane su matse shi.
10 Kwa kujha aponisi bhingi, ili kila munu jha ajhele ni malombosi ajhele ni shauku jha kun'fikila ili an'kamulayi.
Gama ya warkar da mutane da yawa, masu cututtuka suka yi ta ƙoƙarin zuwa gaba, don su taɓa shi.
11 Popoha pala roho bhachafu bho bhikambona, bhabinili pasi mbele jha muene ni kuleta na bhajobhili, “Bhebhe ndo Mwana ghwa k'yara”.
Duk sa’ad da mugayen ruhohi suka gan shi, sai fāɗi a gabansa, su ɗaga murya, su ce, “Kai Ɗan Allah ne.”
12 Akabhakuta kwa msisitizo bhasibhombi amanyikanikayi.
Amma yakan tsawata musu, kada su shaida ko wane ne shi.
13 Akalota panani pa kid'onda, na akabhakuta bha abhalondeghe, na bhakabhoka.
Yesu ya hau gefen wani dutse, ya kira waɗanda yake so, suka kuma zo wurinsa.
14 Akakabhachagula kumi ni bhabhele (abhakutili mitume), ili. kwamba bhajhelayi pamonga ni muene na abhwesiaghe kubhatuma kuhubiri,
Ya naɗa sha biyu, ya kira su manzanni don su kasance tare da shi, domin kuma yă aike su yin wa’azi,
15 ni kujha ni mamlaka gha kubhosya mapepo.
don kuma su sami ikon fitar da aljanu.
16 Na akabhachagula kumi ni bhabhele: Simoni, j'haampelili lihina lya Petro,
Ga sha biyun da ya naɗa. Siman (wanda ya ba shi suna Bitrus);
17 Yakobo mwana ghwa Zebedayo, ni Yohana ndongo munu Yakobo, j'haampelili lihina lya Bonagesi, abhu ndo bhana bha ngurumo,
Yaƙub ɗan Zebedi da kuma ɗan’uwansa Yohanna (ga waɗannan kuwa ya sa musu suna Buwarnajis, wato, “’ya’yan tsawa”);
18 ni Andrea, Filipo, Bartholomayo, Mathayo, Tomaso, Yakobo mwana wa Alfayo, Thadayo, Simoni Mkananayo
Andarawus, Filibus, Bartolomeyu, Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Taddayus, Siman wanda ake kira Zilot,
19 ni Yuda Iskariote, ambaj'he an'saliti.
da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
20 Kisha akalota kunyumba, ni bhumati bhwa bhanu bhakahida pamonga kabhele, hata bhasibhwesi kulya kabhele hata nkate.
Sai Yesu ya shiga wani gida, taro kuma ya sāke haɗuwa, har shi da almajiransa ma ba su sami damar cin abinci ba.
21 Familia jha muene bho bhapeliki habari ejhu bhakalota kun'kamula, kwani bhajobhili, “Arukibhu ni kuhala”.
Da’yan’uwansa suka sami wannan labari, sai suka tafi don su dawo da shi, suna cewa, “Ai, ya haukace.”
22 Bhaandishi bhabhahidili kuh'oma Yerusalemu bhajobhili, “Apagewe ni Beelzebuli,” ni, “Kwan'tawala ghwa mapepo ibhosya mapepo”.
Malaman dokokin da suka zo daga Urushalima suka ce, “Ai, yana da Be’elzebub! Da ikon sarkin aljanu yake fitar da aljanu.”
23 Yesu akabhakuta kwa muene ni kujobha nabhu kwa mifuanu, “Jinsi gani lisyetani kibhwesiayi kumbosya lisyetani?
Sai Yesu ya kira su, ya yi musu magana da misalai ya ce, “Yaya Shaiɗan zai fitar da Shaiɗan?
24 Kama bhufalme bhugawanyiki bhwene, bhufalme obhu ghwibhwesya lepi kujhema.
In mulki yana gāba da kansa, wannan mulki ba zai tsaya ba.
25 Kama nyumba jhigabhwanyiki jhiene, jhibhwesya lepi kujhema.
In gida yana gāba da kansa, wannan gida ba zai tsaya ba.
26 Kama lisyetani libeta kujhinuka kinyume kyake liene, libhwesya lepi kujhema, na kubetakujha lifikili mwisho bhwake.
In kuwa Shaiɗan yana gāba da kansa, ya kuma rabu biyu, ba zai tsaya ba, ƙarshensa ya zo ke nan.
27 Lakini ajhelepi hata mmonga jhaibhwesya kujhingila mugati mu nyumba jha munu mwenye nghofu ni kuheja fenu fya muene bila kunfunga mwenye nghofu hoti, na Kisha ni kubhonganiya Kya kijhele mu nyumba.
Tabbatacce, ba mai shiga gidan mai ƙarfi yă kwashe dukiyarsa, sai bayan ya daure mai ƙarfin, sa’an nan zai iya yin fashin gidansa.
28 Bhukweli nikabhajobhela, dhambi syoha. sya bhana bha bhanu sibetakusamehebhwa, pamonga ni kufufulibhwa ambasyo bhitamka,
Gaskiya nake gaya muku, za a gafarta duk zunubai da kuma saɓon mutane suka yi.
29 lakini jhejhioha jhaibeta kun'situ Roho Mtakatifu ibetalepi kusamehebhwa kamwe bali ajhele ni hatia jha dhambi jha milele”. (aiōn , aiōnios )
Amma duk wanda ya saɓi Ruhu Mai Tsarki, ba za a taɓa gafara masa ba. Ya aikata madawwamin zunubi ke nan.” (aiōn , aiōnios )
30 Yesu alijobhili ele kwa ndabha bhajobhaghe, “Ajhe ni roho bhachafu”.
Ya faɗi haka domin suna cewa, “Yana da mugun ruhu.”
31 Kisha nyinamunu ni bhalongomunu bhakahida ni kujhema kwibhala. Bhakan'tuma munu kun'kuta.
Sai mahaifiyar Yesu tare da’yan’uwansa suka iso. Suna tsaye a waje, sai suka aiki wani ciki yă kira shi.
32 Ni bhumati bhwa bhanu bhwabhujhele bhutamili karibu nu muene bhakan'jobhela, “Nyinu aku ni bhalongobhu bhajhe kwibhala, na bhikulonda bhebhe”.
Taron yana zaune kewaye da shi, sai suka ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna waje, suna nemanka.”
33 Akabhajibu, “Niani nyina bhangu ni ndongobhangu?”
Ya yi tambaya ya ce, “Su wane ne mahaifiyata, da’yan’uwana?”
34 Akabhalanga bhabhatamili bhan'syonguiki ni kujobha, Lakini, Langayi, abha ndo bha nyina bhangu ni bhalongobhangu!
Sai ya dubi waɗanda suke zaune kewaye da shi ya ce, “Ga mahaifiyata da’yan’uwana!
35 Jhejhioha j'haibhomba mapenzi gha K'yara, munu oj'hu ndo ndongobhangu, ndo nd'ombo bhangu, ni nyina bhangu”.
Duk wanda yake aikata nufin Allah, shi ne ɗan’uwana, da’yar’uwata, da kuma mahaifiyata.”