< Matai 13 >

1 Eilinchuva eilyo uYesu akhakhegha munyumba akhaluta khulukhanji khu nyanja akhatama.
A waccan rana Yesu ya fito daga gida ya zauna a gefen teku.
2 Avanu avinghi valundamine, vakhanchungula, umwene pwakhingile mumbwato akhatama mughati. Avanu avinghi pwu vakheima khulukanji khu nyanja.
Taro mai yawan gaske kuwa suka kewaye shi, sai ya shiga cikin kwalekwale ya zauna. Dukan taron kuwa na tsaye a bakin tekun.
3 Pwu akhavavula ifinu finghi aliekhuhwananincha ni fihwani, alikhunchova, “Mlole, umbyalie alutiele khuvyala.
Sai Yesu ya fada masu abubuwa da yawa cikin misalai. Ya ce, “Wani mai shuka, ya tafi yayi shuka.
4 Aliekhuvyale ienchinghe iesekhe nchiliekhugwa mu njiela pwu fikhincha ifideghe fikhahola.
Da yayi shukar, wadansu irin suka fadi a kan hanya, sai tsunsaye suka zo suka cinye su.
5 Inchinghe nchikhagwa palunalawe, incho sanchakhave ung'anga mwingi ukhuta nchimelaghe. Nchikhamela ulwa khuva ung'anga gwale indebe.
Wadansu irin kuwa suka fadi a kan duwatsu, wurin da babu kasa. Nan da nan sai suka tsira, domin kasar babu zurfi.
6 Pwu ulunchuva lwavile lwivala lukhanyanya iemilela ulwa khuva gyale pakanya ung'anga gwale iedebe pwu nchikhuma.
Amma da rana ta taso, sai suka yankwane domin ba su yi saiwa ba, suka kuwa bushe suka zube.
7 Iembeyu inchienghe nchagwile mumintwinyo. Eimitwinyo gheikhakhula ghekhava mitali ukhulutielila inchene pwu nchikhalemwa ukhukhula.
Wasu irin kuwa suka fada a cikin kayayuwa. Kayayuwan kuwa suka shake su.
8 Iembeyu inchienghe nchikhagwa mung'anga unonu, nchikhamela nukhuhupa, inchienghe nchikhahola mala mia moja, inchinge sitini, inchingi salasini.
Wasu irin kuwa suka fada a wuri mai kyau suka ba da tsaba, wani ya ba da dari, wasu sitin, wasu kuma talatin.
9 Umwene uvyalienie mbulukhutu inchakhupulikha apuliekhaghe.
Duk mai kunnen ji, bari ya ji.
10 Avankhongi va mwene vakhincha vakhambuncha u Yesu, “Khinu khiekhi inkhewienchova na vanu wienchova nifiehwaniehencho?”
Almajiran suka zo suka ce ma Yesu, “Don me ka ke yi wa taron magana da misali?”
11 UYesu akhavanda akhata, “Umwe mkhavile ukhunchimanya inchilikhuvutitu incha ludeva ulwa khukyanya, avene savakavile.
Yesu ya amsa ya ce masu, “An baku 'yanci ku fahimci asiran mulkin sama, amma gare su ba a bayar ba.
12 Ulwa khuva umwene yuywa alienafwo ifinu uywa vie vieikyongelenchiwa ifinghe, hangha pwiva nafyo ukhulutielila. Uvalievuvule hange nakhikyo alienakyo pwu ipokhiwa kyope.
Domin wanda yake da shi, za a kara masa, zai kuma samu dayawan gaske. Amma duk wanda ba shi da shi, sai a dauke har ma abin da yake dashi.
13 Pwu ninchova nawo khufikhwani ulwa khuva vangalolaghe savakhalolaghe. Hanghe vangapuliekhaghe valekhe ukhupuliekha, hanghe valekhaghe ukhunchimanya.
Saboda haka na yi masu magana cikin misalai, amma ko da ya ke sun gani, duk da haka ba su gani ba. Kuma ko da yake sun ji, hakika ba su ji ba, balle ma su fahimta.
14 Eilimenyu lya nyamalago uIsaya lievombikhe khuvene pwu lita, ukhuphulikha mpulikhagha hanghe samukhanchimanyaghe.
A gare su ne annabcin Ishaya ya cika, wanda yake cewa, “Game da sauraro zaku saurara, amma ba za ku fahimta ba. Game da gani kuma za ku kalla, amma ba za ku gane ba.
15 Ulwa khuva ienumbula incha vanu ava nchivile nchitu, niembulukhuto nchavo sanchipulikha vunonu, namiho gha vene vasisiliele, ukhuta valekhe ukhulola na miho ghavene, vakhaphulikha ni mbulukhuto nchavene, vakhanchimanya ni numbula nchavene vakhasyetukha, une nikhavapokha.”
Domin zuciyar mutanen nan ta duhunta, sun taurare ga saurare, kuma sun rufe idanunsu domin kada su gani da idanunsu, ko kuwa su ji da kunnuwansu, ko kuwa su fahimta da zukatansu, saboda su juyo kuma in warkar da su'.
16 Musayiwe ulwa khuva amiho gheinyo ghilola, nie mbulukhuto ncheinyo nchiepuliekha.
Amma idanunku masu albarka ne, domin sun gani, haka ma kunnuwanku, domin sun ji.
17 Mwiedhiekhaghe nikhuvavula, avanya malagho avingi na vanu avanya lwiedhikho vanogwagwa ukhunchivona nchila unchumukhunchivono. Valemilwe ukhunchievona, vanoghilwe ukhuphulikha imbombo iela inchumupuliekha, savakhapuliekha.
Hakika ina gaya muku, annabawa da mutane dayawa masu aldalci sun yi marmarin ganin abin da kuka gani, amma ba su sami ganin su ba. Sun yi marmarin jin abin da kuka ji, ba su kuwa ji su ba.
18 Pwu mupuliekhaghe lieno ienongwa iya mbyalii.
Ku saurari misalin nan na mai shuka.
19 Umunu uvieiphuliekha eilimenyu ilya ludeva ulwa khukyanya alekhaghe ukhuliemanya, umbivi pwu ikhwincha itola eiliekhavyaliwe munumbula mumwene. Eiyi yu mbeyu iyavyaliwe munundukhanji munjila.
Idan wani ya ji maganar mulkin sama amma bai fahimce ta ba, sai mugun nan ya zo ya kwace abinda aka shuka a zuciyarsa. Wannan shine irin da aka shuka a kan hanya.
20 Uvya vyaliwe mundunalawe vie ule uvyaliephokhiele ielimenyo nukhuhovoka.
Shi wanda aka shuka akan duwatsu, shine wanda ya ji maganar ya kuma karbe ta da murna nan da nan.
21 Alivale eimilela mughati mumwene, lietama unsiekhe iendebe. Pwu yienghahumile ietabu apanghe ukhuhanghayiekha khu nongwa ya liemenyu, umwene pwu iviepha iembeive.
Duk da haka, bai yi karfi cikin ta ba kuma nan ba da dadaiwa ba. Da wahala da tsanani suka taso saboda maganar, sai ya yi tuntube nan da nan.
22 Uvieavyaliwe mumintwinyo, uyuo vieiphulikha eilimenyu iekwaghana ni mbombo incha nkhilunga nifwa vunongwe uwankhielungha pwu nchikhu mpelela ukhuta ielimenyu lielekhe ukhupa iesekhe. (aiōn g165)
Shi wanda aka shuka a cikin kayayuwa wannan shine wanda ya ji maganar, amma dawainiyar duniya da kuma yaudarar dukiya suka shake maganar, sai ya kasa ba da 'ya'ya. (aiōn g165)
23 Uviavyaliwe mung'anga unonu. Uyuo veihola isekhe na vienchiholagha isekhe nchunyingi mala mia, iyeinge sitini, iyeingi salasini.”
Shi wanda aka shuka a kasa mai kyau, wannan shine wanda ya ji maganar, ya kuma fahimce ta. Wannan shine wanda ba da 'ya'ya da gaske; wadansu ribi dari, wadansu sittin, wasu kuma talatin.”
24 UYesu akhavapha eikhikhwani eikhinghe. Akhanchova, “Uludeva lwa khukyanya luhwanine numu yuywa avyalile iembeyu mukyalo kya mwene.
Yesu ya sake ba su wani misali, yana cewa “Za a kwatanta mulkin sama da wani mutum wanda ya shuka iri mai kyau a gona.
25 Vuvaghonelile avanu pwu vakhancha avalughu vamwene akhavyale amanyasi munganu vakhahegha vakhaghodokha.
Amma da mutane suka yi barci, magabcin sa ya zo ya shuka ciyayi a cikin alkamar, ya kuwa yi tafiyarsa.
26 Ingano yiekhamela nukhuhupha, na ghamanyasi ghope ghakhamela.
Sa'adda suka yi toho suka kuma ba da tsaba, sai ciyayin suka bayyana.
27 Avavombi va nyakyalo vakhincha vakhambuncha unyakyalo vakhata, 'Khikhi sawauyale iembeyu einonu mukyalo kyako? Khihumile khikhi lino mbona ghamelile amanyasi?
Bayin mai gonar kuwa suka zo suka ce masa, maigida, ashe ba iri mai kyau ka shuka a gonarka ba? ya ya aka yi ta kasance da ciyayi?
28 Akhavavula akhata, undughu avombile imbombo inchi.' Avavomba mbombo vakhambola vakhata, “Lino wienogwa tukhakhupule?”
Ya ce masu, “Magabci ne ya yi wannan”. Sai bayin suka ce masa, 'kana so mu je mu tuge su ne?'
29 Unyakyalo akhanchova akhata, 'Mwielekhelwe, ukhuluta khukupula, ulwa khuva vumukhupula amanyasi pwu mukhupulagha nayie ngano pwu paninie.
Mai gonar ya ce, 'A'a, kada a garin tuge ciyayin, ku tuge tare da alkamar.
30 Mughalekhe ghakhula pupaninie ukhudugha upwakhiva gwifikha unsiekhi ugwakhubena. Unsiekhi ugwakhubena niela vavula aviebena ukhuta, 'Mutale ukhunkhupula amanyasi mughakhunghe mumwoto, pwu mulundamanie einganu tuviekhe mukhibana kyango.”
Bari dukan su su girma tare har lokacin girbi, a lokacin girbin zan gaya wa masu girbin, “Ku tuge ciyayin da farko a daura su dami dami sai a kona su, amma a tara alkamar a kai rumbunana.'”
31 U Yesu akhavavula ikhikhwani hincho ikhinghe. Akhata, “'Uludeve ulwa khukyanya lukhwanine nie mbeyu iya haladali(iendebe nno) yienyo umunu atoliele akhaluta kuvyala mukyalo ikya mwene.
Sai Yesu ya sake yin magana da su cikin misalai, yana cewa “Za a kwatanta mulkin sama da kwayar mustad, wanda wani mutum ya shuka a lambunsa.
32 Eimbeyu eiye nini eno(ndebe) ukhulutilila imbeyu inchinghe nchoni. Vuyimela nukhukhula pwu yiekhula yive iembiekhi imbaha ukhulutilila ambiekhi eghienghe mukyalo pwu ifidege ifya munkyanya vikwinchaga vikwemaga nukhughataluka pakyanya pa mbikhi finchengagha nuvufumba mumaswatu gha mbikhe.”
Wannan iri shine mafi kankanta cikin dukan iri. Amma bayan ya yi girma, sai ya fi dukan ganyaye dake lambun. Ya zama itace, har ma tsuntsayen sama su yi sheka a rassansa.”
33 Akhavapha ikhikhwananincho eikhinghe akhata. “Uludeva ulwa khukyanya lukyanine nie khinu ikhilulile khikyo undala atolile akhapima ifiphimielo fidatu akhahanjania mumbutine woni vukhatutuma.
Yesu ya sake fada masu wani misali. “Za a kwatanta mulkin sama da yisti da mace takan dauka ta kwaba gari da shi mudu uku har sai ya yi kumburi.”
34 Nchoni ienchi uYesu anchovile pavanu avinghi nukhuhwananincha ifihwani. Ukhulekha ifyakhuhwananincha pwu salikhunchova khinu.
Duk wadannan abubuwa Yesu ya fada wa taron cikin misalai. Babu abinda ya fada masu da ba a cikin misali ba.
35 Ukhuva nchila inchanchoviwe navanyamalagho nchivonekhaghe, upwu inchova, “Uyunikyama undomo gwangho ukhuchova khufihwani. Uyuninchova imbombo nchincho nchikhale khuvutitu ukhuhuva khuvutenghulilo uwa khilunga.”
Wannan ya kasance ne domin abinda annabin ya fada ya zama gaskiya, da ya ce, “Zan buda bakina da misali. In fadi abubuwan da ke boye tun daga halittar duniya.”
36 Pwu uYesu akhavalekha avanu vinghi akhaghodokha khumyave. Pwu avakhongi avamwene vakhankongha vakhata, “Utuvule vunonu ikhihwani ikyamasi mukyalo.”
Sai Yesu ya bar taron ya shiga cikin gida. Amajiransa suka zo wurin sa suka ce, “Ka fasarta mana misalan nan a kan ciyayin da ke gonar”
37 U Yesu akhavanda akhata, “Uvie ivyala iembeyu inonu vei mwana va Adamu.
Yesu ya amsa kuma ya ce, “Shi wanda ya shuka iri mai kyau Dan Mutum ne.
38 Eikyalo kyu khilunga; imbeyu einonu vuvana avakhuludeva. na manyasi vuvana ava ndughu untavangwa, nuu mbivi uviavyalile vei setano.
Gonar kuwa duniya ce; iri mai kyau kuma sune 'ya'yan mulkin. Ciyayin kuma sune 'ya'yan mugun,
39 Uvubeni vuvusililo uwa khilunga, aviebena vuvasuhwa va nghuluve. (aiōn g165)
magabcin da ya shuka su kuma shaidan ne. Girbin shine karshen duniya, kuma masu girbin sune mala'iku. (aiōn g165)
40 Amanyasi vughilundama nukhu nyanya mu mwoto, vuyilava eiwo khuvumalilo uwa khilunga. (aiōn g165)
Saboda haka, kamar yadda aka tara ciyayin aka kona su da wuta, haka ma zai faru a karshen duniya. (aiōn g165)
41 Umwana va Adamu alasuha avasung'wa vamwene, ukhwincha khuluondamania ukhuhuma khuludeva ulwa mwene imbombo nchoni inchikhapelagha imbivi na voni avakhavombagha inchambivi.
Dan Mutum zai aiki mala'ikunsa, kuma su tara dukan abubuwan da ke sa zunubi daga cikin mulkinsa, da kuma wadanda su ka yi aikin mugunta.
42 Voni valalahiwa mundighuli eilya mwoto, ukhwa khukhulava nikhililo nukhuheveta amino.
Za su jefa su cikin korama ta wuta, inda za a yi kuka da cizon hakora.
43 Pwu avanu vavo vavombagha inonu valang'ala ndielinchuva khuludeva ulwa Dada vavo. Uvyalieni mbulukhuto aphuliekhaghe.
Sa'an nan ne mutane masu adalci za su haskaka kamar rana a mulkin Ubansu. Bari mai kunnen ji, ya ji.
44 Uludeva ulwa khukyanya luliehani niekhiebana khikyo khiefihiele mukyalo. Umunu akhakhievona akhafiha. Munduhekhelo ulwa mwene pwu akhaluta khwighuncha fyoni fifwo akhale nafwo, nukhughula eikyalo.
Mulkin sama kamar dukiya ce da ke boye a gona. Mutum ya samu sai ya boye ta, ya tafi cikin murna, ya sayar da mallakarsa kuma ya sayi filin.
45 Hange uludeva ulwa khukyanya luleindumunu unchulusi uvieilonda ulutalama ulunonu ulwa khukhava indalama inchiluteilile.
Haka ma za a kwatanta mulkin sama da wani attajiri mai neman Lu'ulu'ai masu daraja.
46 Aviele akhaviele uluntalama ulunonu ulualondagha, ankhaluta ankhaghuncha iefyuale nafyo fyoni ankhanchighula ulutalama uluanoghielwe.
Da ya sami lu'ulu'u daya mai darajar gaske, ya je ya sayar da dukan mallakarsa ya kuma saye shi.
47 Uludeva ulwa khukyanya luliehaniele ni nyafu inchilakhiwa munyanja, pwu nchi lundamania khila khinu eikhiliemaghasi.
Haka kuma, za a kwatanta mulkin sama da taru da aka jefa cikin teku, ya kuwa tara hallitu iri-iri.
48 Vunchidieghile avalovi pwu vikhweghela khulu nkhanji vitama pasi, pwu visalula iefinonu vinhola viveikha mu fyombo, ifisafielondiwa pwu viekhufietagha khuvutali.
Da ya cika, sai masuntan suka jawo shi bakin tekun. Sai suka zauna suka tara kyawawan abubuwan a taska, amma munanan abubuwan, suka watsar da su.
49 Vuyielava eiwo eilinchuva eilya khusiliela eikhilunga. avasuhwa valukhumila, valavakhencha avavomba mbivi voni mughati mbavo vivomba ienonu. (aiōn g165)
Haka zai kasance a karshen duniya. Mala'iku za su zo su ware miyagu daga cikin masu adalci. (aiōn g165)
50 Pwu valavatagha mundighuli ilya mwoto, pwu khulava nikhilielo nukhu kheveta amino.
Za su jefa su cikin korama ta wuta, inda za a yi kuka da cizon hakora.
51 U Yesu akhavavuncha munchimanyile imbombo nchoni? Avankhongi va mwene vakhanda vakhata, “Ena.”
Kun fahimci dukan wadannan abubuwa? Amajiran suka ce da shi, “I”.
52 Pwu u Yesu ankhavavula akhata, “'Khila nkhalani yuoywa aviele nkhonghi va ludeva ulya khukyanya, akhwanine nunyanyumba uvie ihumya mukhibana kyamwene iehomya ifinu ifiepya nie finkhulu.”
Sai Yesu ya ce masu, “Saboda haka kowane malamin attaura da ya zama almajirin mulkin sama, yana kamar mutum mai gida wanda ya zaro tsoho da sobon abu daga taskarsa.”
53 U Yesu wa maliele iefikhwanie kheincho, akhakhegha pala upwuale.
Daga nan, sa'adda Yesu ya kammala ba da wadanan misalai, sai ya tafi ya bar wurin.
54 U Yesu wanchifikhe khukhielunga eikya khumyave ukhu aliekhunchikhuvamanyisya avanu muntembiele. Pwu valiekhudhegha valiekhuta uyuo atoliele ndakhu uluhala uolu nie fidhehgo iefii?
Sai Yesu ya shiga yankinsa ya koyar da mutane a masujadarsu. Saboda haka suka yi mamaki suna cewa, “Daga ina wannan mutumin ya sami hikimarsa da al'ajibai?
55 Umunu uyou samwana vaselemala? uMariamu ndasavie vanina? Avalokhololwe savuva Yakobo, Yusufu, Simoni nu Yuda?
Wannan mutumin ba dan masassakin nan ba ne? Ba kuma sunan mahaifiyarsa Maryamu ba? Ba Kuma 'yan'uwansa sune, Yakubu da Yusufu da Saminu da kuma Yahuza ba?
56 Navahanchave tulie navo apha pakhaya? Khumbe umunu uyou anchiwene ndhakhu ienchi nchoni?”.
Ba 'yan'uwansa mata na tare da mu ba? To daga ina wannan mutumin ya sami dukan wadannnan abubuwa?
57 Vakhaviphinchana. U Yesu akhavavula, “Unyamulagho sakhalemwe ukhudwadiwa. Khumyave sakhadwadiwe na mumu nkhielunga ikya myiave.
Suka bata rai saboda shi. Amma Yesu ya ce masu, “Ai annabi bai rasa daraja sai dai ko a garinsa da kuma cikin iyalinsa.
58 Pwu akhilekhelwa ukhuvomba ifiedhekho finghi khumyave ulwa khuva savaliekhumwiedhikha.
Kuma bai yi al'ajibai dayawa a can ba saboda rashin bangaskiyarsu.

< Matai 13 >