< Avaefeso 1 >
1 Paulo, avasikhiwa va Yeesu nuogane vamwene o Nguluve, avavekhiwe khumbombo ya hutwa navovo vile Efeso vedesi khwa Kristi.
Bulus, manzon Yesu Almasihu ta wurin nufin Allah, zuwa ga kebabbu na Allah da ke a Afisa wanda suke aminci cikin Yesu.
2 Oluhungo luve hyolyomwe olunchehecho khwa Daada O Yeesu Kristi.
Bari alheri ya kasance da ku, da salama daga wurin Allah Ubanmu da Ubangijinmu Yesu Almasihu.
3 Unguluve nu Daada uvakholo deva u Yeesu Kelesti aginiwage vemwene atusayile khulusayo lywa khenumbula khosehemu ya khokyanya kho Yeesu Kelesiti.
Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Almasihu. Shine ya albarkace mu da kowanne albarku na ruhaniya da ke cikin sammai cikin Almasihu.
4 Wusaheuombiwe chelonga Unguluve ahatuchangwile ufye yufye fule nu unonchehencho khwa Khelesiti. Ahatunchagwile ufye tuvenchage vavalanche tolekhe ukholaumki khya Kelesiti.
Kafin halitar duniya, Allah ya zabe mu da muka ba da gaskiya cikin Yesu. Ya zabe mu domin mu yi zaman tsarki da rayuwar da babu aibu a gabansa.
5 Khologano lya Nguluve ahtonchagwile ohoma khovotengololo ilitoliwe nuvana vamwene u Yeesu Kelesiti.
Cikin kauna Allah ya kaddara ya dauke mu mu zama yayansa ta wurin Yesu almasihu. Ya yi wannan domin ya gamshe shi ya yi abin da ya ke so.
6 Amutokeo gamwene Unguluve tuhopa isifa nulohongo nuvotukufu wa mwene. Ekho kihyene ekhokatupile vole huhyela ya ogane vamwene.
Sakamakon shine Allah ya karbi yabo domin daukakan alherinsa. Wannan shine abinda ya ba mu hannu sake ta wurin kaunataccensa.
7 Ulwakuva hogane vamwene tugomboliwe ukhugendela mkisa yuamwene, olusye helo lya mbivi tulenalyo elyo hosabu ya votayeli walohongo lya mwene.
Gama cikin kaunataccensa aka fanshe mu ta wurin jininsa, da gafarar zunubai ta wurin wadataccen alherinsa.
8 Akavombile olohongo uvo hujili yeto nebusara nu luhara.
Ya ba da wannan alherin a yalwace cikin dukan hikima da fahimta.
9 Unguluve ahovombile uhota uamanyehe hulyofye avolyeli vovwa wofihile no pango, ohohomana novosongo wagati mwa kelesiti.
Allah ya bayyana mana gaskiyar al'amarin da aka boye na shirinsa, ta wurin abin da yake so ya nuna cikin Almasihu.
10 Usehe gotimelie opango gwamwene, Unguluve ilondamanya pupaninye hela henu kya hukinya nehopakyanya pahelunga igani mwa kelesiti.
Idan lokaci ya yi na kammala shirinsa, Allah zai kawo dukan abubuwan da ke sama da kasa cikin Yesu.
11 Usehe ugwa Kelesite tohaviletonchaguliwe nuhosuhudela osehe. Wosangofihe yoni eyeyeho mine nupango uyiwomba ifinu lyoni ifunu vyakuswelu igagane vamwene.
An zabe mu cikin Almasihu mu zama abin gado na Allah. Ya yi mana wannan shirin tun da cikin shirin sa, shi mai yin dukan abu ta dalilin nufinsa.
12 Unguluve ahavombile evetovepo ilitowesye uhuvepo ndoginwo lyamwene. Tohale vahyanja uhova na vojasili egati mwa Kelesiti.
Allah ya yi haka saboda mu rayu domin yabon daukakarsa. Mune na farko da muka sami bege cikin Almasihu.
13 Yehale enjela ya Kelesiti uhuta mpolehe elimenyu lya lyeli, einjili ya wosiwa wenyo honjela ya Kelesiti. Yehale nohota omuemwe musangini nuhutwa ong'uli gwa Enumbula Ombalanche vyaginwe.
A cikin Almasihu ne kuma kuka samu jin maganar gaskiya, bisharan cetonku ta wurin Yesu. A cikinsa ne kuka bada gaskiya aka hatimce ku da Ruhu Mai Tsarki wanda aka alkawarta.
14 Enumbula yasamimi ya uvolisi weto impaha totavale ipaka upo yaha vuvoneha. Eye yehale hosifa yaloginwo iyamwene.
Ruhun shine tabbacin gadonmu kafin mu kai ga samunsa. Wannan don yabon daukakarsa ne.
15 Ulwakuva eye, uhuhuma uwuka votopolike uhohusu ulwoleho lyenyo egati mwa Untwa Yeesu ukhuhusu ulogano lyenyo hovoni avatengiwe homwine.
Sabo da haka, tun lokacin da na ji labarin bangaskiyarku cikin Ubangiji Yesu da kaunar ku zuwa dukan wadanda aka kebe dominsa.
16 Sanene valekhile ukhoginya Unguluve khusababu yenyo nohovataja kholesayo lyango.
Ban fasa tunawa da ku ba ina addu'a saboda ku cikin addu'o'ina.
17 Nikhovadava ukhuta Unguluve no Daada veto Uyeesu Kelesiti, Udaada va lyodwado, tuhovapa umepo uvaluhara, uluvunchelo lya vofahamu lyamwene.
Ina addu'a da cewa Allah Ubangijinmu Yesu Almasihu, Uban daraja, ya ba ku ruhun basira da wahayin saninsa.
18 Nidava ukhuta amiho genyo gamunumbula gavehiwe ulumuli hulyomwe ilimo lomanye wowolehu uvojasili wakhyelangiwa hyulwomwe. Nidova mlomanye ohuta uvatayeli wavodwado nuvulisi wa mwene vavo vahatenyiwe hujili ya mwene.
Ina addu'a idanun zuciyarku su bude domin ku san tabacin kiranku. Ina addu'a dominku san arzikin mulkin gadonsa cikin wadanda aka kebe dominsa.
19 Nidova ohota mlomanye uvuvana vosidile ingovu nchizidile egate dwofye tole lenetumaini uvovovaha wohomine nohivomba embombo minyofu ncha mwene.
Ina addu'a ku san ikon nan nasa mai girma mara iyaka da ke cikin mu da muka ba da gaskiya. Wannan girman yana ta wurin aikin karfin ikonsa ne.
20 Ngangomaha agavombihe mmbombo ya Kelesiti wakati Unguluve achosinche uhoma huvofye nuhutamuha mwavoho gamwene hohevoha ekhyahege musehemu ya Nguluve.
Wannan shine ikon da ya yi aiki cikin Almasihu lokacin da Allah ya tashe shi daga matattu ya sa shi a hannun damansa cikin sammai.
21 Ahatamih Ukelesiti hyokyanya hutaki huvotawala, nahylalitawa elianchoviwa. ahatamihe Unguluve sio huwakati uwa khosehe ogoguhyi cha leno. (aiōn )
Ya sanya shi bisa birbishin dukan sarauta, iko, mulki, karfi, da kowanne irin suna. Ya sanya Almasihu ba a wannan zamanin kadai ba, amma da zamani mai zuwa. (aiōn )
22 Unguluve afidwanchinche paasi pamalonde ga Nguluve ambombile uhuva pakyonya pafinu nyoni mkanisa.
Allah ya saka dukan abubuwa a karkashin kafafun Almasihu. Ya sa shi shugaban dukan abubuwa a cikin ikilisiya.
23 Elikanisa khota gombele gwa mwene uvokamilifu wamwene uwowidega ifinu fyoni mjela nchooni.
Ikilisiya jikinsa ne, cikarsa wanda ya cika dukan abubuwa cikin kowacce hanya.