< Mathayo 26 >
1 Omwanya ogwo Yesu ejile amalisha okwaika emisango jone ejo, abhabhwiliye abheigisibhwa bhaye,
Sa’ad da Yesu ya gama faɗin dukan waɗannan abubuwa, sai ya ce wa almajiransa,
2 mumenyele ati jasigalao nsiku ebhili nibhao isikukuu ya ipasaka, omwana wo munu alisosibhwa koleleki abhambwe ku musalabha.”
“Kamar yadda kuka sani, Bikin Ƙetarewa sauran kwana biyu, za a kuma ba da Ɗan Mutum don a gicciye shi.”
3 Gunu gwalubhie abhakulu bha bhagabhisi na bhakaluka bha bhanu bhekofyanyishe amwi kubhwikalo bha omugabhisi omukulu unu atogwaga kayafa.
Sai manyan firistoci da dattawan mutane, suka taru a fadan babban firist, mai suna Kayifas,
4 Kwa amwi bhalomele inama yo kumugwata Yesu kwa ibhisike no kumwita.
suka ƙulla shawara su kama Yesu da makirci, su kuma kashe shi.
5 kwo kubha abhaikile ati,”Jitakabhonekene mu mwanya gwa isikuku, koleleki yasiga kwibhukao inyombo agati mu bhanu.
Suka ce, “Amma ba a lokacin Biki ba, don kada mutane su tā da rikici.”
6 Omwanya gunu Yesu aligali mu Bethania mu nyumba ya Simoni omugenge.
Yayinda Yesu yake a Betani, a gidan wani mutumin da ake kira Siman Kuturu,
7 aliga enyolosisye kumeja, omugasi umwi ejile kumwene aliga agegele likopo lya Alabhasita elyo lyaliga Lili na mafuta go bhugusi bhunene, agetululie ingulu ku mutwe gwae.
wata mace ta zo wurinsa da wani ɗan tulun alabasta na turaren mai tsada sosai, wanda ta zuba a kansa a lokacin da yake cin abinci.
8 Nawe abhweigisibhwa bhae bhejile bhalola omusango ogwo, bhabhiiliwe no kwaika ati niki isonga ya okufyilwamo kutya?
Sa’ad da almajiransa suka ga wannan, sai suka yi fushi. Suka ce, “Wannan almubazzaranci fa!
9 Ganu, gakengene okugusibhwa kwo bhugusi bhunene na nibhayanwa abhataka.”
Wannan turare ai, da an sayar da shi da kuɗi mai yawa a ba matalauta kuɗin.”
10 Nawe Yesu aliga amenyele linu, abhabhwilie, ati “kulwa ki omunyasya omugasi unu? Okubha akola Chinu chakisi kwanye.
Sane da wannan, Yesu ya ce musu, “Me ya sa kuke damun macen nan? Ta yi mini abu mai kyau ne.
11 Abhataka mu nabho siku jone, nawe mutalibha aamwi nanye kusiku.
Matalauta za su kasance tare da ku kullum, amma ni ba zan kasance tare da ku kullum ba.
12 Okubha anu anyitilie amafuta ingulu yo mubhili gwani, akolele kutyo kulwo kusikwa kwani.
Sa’ad da ta zuba turaren nan a jikina, ta shirya ni ne don jana’izata.
13 Nichimali enibhabhwila ati, wona wona echigambo chinu chilyaikwa muchalo chone echikolwa echo akola omugasi unu, one chilibha nichaikwa kulwo kumwichuka.”
Gaskiya nake gaya muku, duk inda aka yi wa’azin bisharan nan a duniya duka, abin da matan nan ta yi, za a riƙa faɗarsa don tunawa da ita.”
14 Mbe niwo oumwi wa bhaliya ekumi na bhabhili, unu atogwaga Yuda Iskariote, agendele kubhakulu bha bhagabhisi
Sai ɗaya daga cikin Sha Biyun nan, wanda ake kira Yahuda Iskariyot, ya je wurin manyan firistoci
15 naika ati,”Omunanaki nikamulomela iniku?” Nibhamulengela Yuda ebhibhala makumi gasatu ebhya jiyela.
ya ce, “Me za ku ba ni, in na bashe shi gare ku?” Sai suka ƙirga masa kuɗi azurfa talatin.
16 Okwambila omwanya ogwo ayenjele omwanya gwo okumulomela iniku.
Daga wannan lokaci, Yahuda ya yi ta neman zarafin da zai miƙa shi.
17 Mbe kulusiku olwo kwamba lunu lutalimo chifwimbya, abheigisibhwa bhamulubhile Yesu nibhaikana ati, “Akiao wenda chikwilabhile ulye ebhilyo bhya Ipasaka?”
A rana ta fari ta Bikin Burodi Marar Yisti, sai almajiran suka zo wurin Yesu suka yi tambaya suka ce, “Ina kake so mu je mu shirya maka wurin da za ka ci Bikin Ƙetarewa?”
18 Nabhabhwila ati, “nimugende mumusi ku munu mulebhe na mumubhwile ati, Omwiigisha aika ati 'Omwanya gwani gwajokukinga. Enijo okukumisha Ipasaka amwi na abheigisibhwa bhani mu nyumba yao.'”
Ya amsa ya ce, “Ku shiga gari wurin wāne, ku ce masa, ‘Malam ya ce, lokacina ya yi kusa. Zan ci Bikin Ƙetarewa tare da almajiraina a gidanka.’”
19 Abheigisibhwa bhakolele lwa kutyo Yesu abhalagile, na bhelabhile ebhilyo ebhya ipsaka.
Saboda haka almajiran suka yi yadda Yesu ya umarce su, suka kuwa shirya Bikin Ƙetarewa.
20 Yejile yakinga kegolo, eyanjile okulya ebhilyo amwi na bhaliya abheigisibhwa ekumi na bhabhili.
Da yamma ta yi, sai Yesu ya zauna don cin abinci tare da Sha Biyun.
21 Anu bhaliga nibhalya ebhilyo, aikile ati, “Ni chimali enibhabhwila ati oumwi wemwe kajo kundomela iniku.”
Yayinda suke cin abinci, sai ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
22 Bhasulubhae muno, bhuli umwi namba okumubhusha, “Ni chimali, atalyanye omukama?”
Suka yi baƙin ciki ƙwarai, suka fara ce masa da ɗaya-ɗaya, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
23 Nabhasubhya ati, “Uliya oyo kakoja okubhoko kwae amwi nanye mumbakuli oyo niwe kajokundomela iniku.
Yesu ya amsa ya ce, “Wanda ya sa hannunsa a kwano tare da ni ne, zai bashe ni.
24 Omwana wo munu kagenda, lwa kutyo andikiwe nawe jilimubhona omunu oyo kamulomela iniku omwana wo munu! Jakabee kisi ku munu oyo akili atakebhuywe.”
Ɗan Mutum zai tafi kamar yadda aka rubuta game da shi. Amma kaiton mutumin da zai bashe Ɗan Mutum! Da ma ba a haifi mutumin nan ba, da ya fi masa.”
25 Yuda, oyo amulomee iniku naika ati, “Si nanye mwiigisaha?” Yesu namubhwila ati, “Waika omusango ogwo awe omwenene.”
Sa’an nan Yahuda, wanda zai bashe shi ya ce, “Tabbatacce ba ni ba ne, ko, Rabbi?” Yesu ya amsa ya ce, “I, kai ma ka fada.”
26 Anu bhaliga nibhalya ebhilyo, Yesu nagega omukate, naguyana amabhando, no kugubheganya. Nabhayana abheigisibhwa bhae naika ati, “Nimugege mulye. gunu Ni mubhili gwani.”
Yayinda suke cikin cin abinci, Yesu ya ɗauki burodi, ya yi godiya ya kuma kakkarya, ya ba wa almajiransa yana cewa, “Ku karɓa ku ci; wannan jikina ne.”
27 Nagega echikombe nasima, nabhayana naika ati nimunywe bhona kuchinu.
Sa’an nan ya ɗauki kwaf, ya yi godiya, ya kuma ba su, yana cewa, “Ku shassha daga cikinsa, dukanku.
28 Kulwo kubha ganu ni manyiga gaindagano yani, inu eitika kulwa bhafu kwo kwiswalililwa ebhibhibhi.
Wannan jinina ne na sabon alkawari, wanda aka zubar saboda mutane da yawa, don gafarar zunubai.
29 Nawe enibhabhwila ati nitalinywa Lindi amatyasho go mujabhibhu gunu kukingila olusiku luliya nilinywa amayaya amwi nemwe mu bhukama bhwa lata wani.”
Ina gaya muku, ba zan ƙara shan ruwan inabin nan ba har sai ranar da zan sha shi sabo tare da ku a mulkin Ubana.”
30 Bhejile bhamala okwimba olwimbho, nibhauluka okugenda ku chima echa mujeituni.
Da suka rera waƙa, sai suka fita, suka tafi Dutsen Zaitun.
31 Mbe niwo Yesu nabhabhwila, mugeta inu emwe bhona omwikujula kulwanye, okubha yandikilwe ati, ndimubhuma omulefi na jinyabhalega ja mwiijo jilinyalabhuka.
Sai Yesu ya ce musu, “A wannan dare, dukanku za ku ja da baya saboda ni, gama a rubuce yake cewa, “‘Zan bugi makiyayin, tumakin garken kuwa za su fasu.’
32 Mbe nawe alibha nasuluka anye nilibhatangatila okugenda Galilaya.”
Amma bayan na tashi, zan sha gabanku zuwa Galili.”
33 Nawe Petro namubhwila ati, “Nolwo kutyo bhalikulema lwa injuno ya amagabho ganu galikubhona, anye ntalikulema.”
Bitrus ya amsa ya ce, “Ko da duka sun ja da baya saboda kai, ba zan taɓa ja da baya ba.”
34 Yesu namusubhya, “Ni chimali enikubhwila ati, mugeta inu ikabha ichali kukokolima, ing'okolome oujo okunyiganilamo okwiya kasatu.”
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya maka, a daren nan, kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
35 Petro namubhwila ati, nolwo kutyo nakabhee kunyiile okufwa nawe, nitakukwigana.” Nabheigisibhwa abhandi nibhaika kutyo
Bitrus ya furta, “Ko da ma zan mutu ne tare da kai, ba zan taɓa yin mūsun saninka ba.” Dukan sauran almajiran ma suka faɗa haka.
36 Mbe nagenda nabho anu atogwaga Getesemane nabhabhwila abheigisibhwa bhae ati, “mwiyanje anu omwanya nigenda eyo no kusabhwa.”
Sa’an nan Yesu ya tafi da almajiransa zuwa wani wurin da ake kira Getsemane, ya ce musu, “Ku zauna nan, in je can in yi addu’a.”
37 Namugega Petro na bhana bhabhili abha Jebhedayo namba okusulubhala no kufwa omutima.
Ya ɗauki Bitrus da’ya’ya biyun nan na Zebedi tare da shi, sai ya fara baƙin ciki, ya kuma damu.
38 Mbe niwo nabhabhwila ati, “omwoyo gwani guli no bhusulubhae bhwafu muno, uti bhokufwa. Mubhega anu nimutengeja amwi nanye.”
Sai ya ce musu, “Raina yana cike da baƙin ciki har kamar zan mutu. Ku dakata a nan, ku kuma yi tsaro tare da ni.”
39 Nagenda imbele kutoto nagwa bhwifumbike, no kusabhwa. Naika ati, “Lata wani labha ejitulikana, echikombe chinu chinyilenge. Lwa kutyo eninda anye atali lwa kutyo wendele awe.”
Da ya yi gaba kaɗan, sai ya fāɗi a ƙasa, ya yi addu’a ya ce, “Ubana, in mai yiwuwa ne, a ɗauke mini wannan kwaf. Amma ba nufina ba, sai naka.”
40 Nabhalubha abheigisibhwa nabhasanga bhamamile bhaongee, namubhwila Petro, “Nikulwaki mutatula okutengeja nanye nolwo esaa limwi?
Sa’an nan ya komo wurin almajiransa, ya tarar suna barci. Ya tambayi Bitrus ya ce, “Ashe, ba za ku iya yin tsaro tare da ni ko na sa’a guda ba?
41 Mutengeje no kusabhwa mutengila mumalegejo. Omwoyo ogwenda, nawe omubhili gulegae.”
Ku yi tsaro, ku kuma yi addu’a, don kada ku fāɗi cikin jarraba. Ruhu yana so, sai dai jiki raunana ne.”
42 Nagenda jae lwa kabhili no kusabhwa naika ati, “Lata wani, labha ligambo linu litakutula okunyilenga na Ni bhusibhusi nichinywele echikombe chinu, elyenda lyao likolwe.
Ya sāke tafiya sau na biyu, ya yi addu’a ya ce, “Ubana, in ba zai yiwu a ɗauke wannan kwaf ba sai na sha shi, to, bari a aikata nufinka.”
43 “Naja Lindi nabhasanga bhaongee, okubha ameso gwebhwe galiga gasitoele.
Da ya dawo, har yanzu ya tarar suna barci, domin idanunsu sun yi nauyi da barci.
44 Niwo nabhasiga lindi nagenda jae. Nasabhwa olwa kasatu naikaga emisango ejoejo
Saboda haka ya sāke barinsu, ya yi addu’a sau na uku, yana maimaita iri abu guda.
45 Mbe neya Yesu nabhalubha abheigisibhwa bwae nabhabhwila ati, “Naoli muchamamilela no kuumula? Nimulole, omwanya gweile omwana wo munu kalomelwa inikun ku mabhoko ga bhebhibhibhi.
Sa’an nan ya komo wurin almajiransa, ya ce musu, “Har yanzu kuna barci kuna hutawa ba? Ga shi, sa’a ta yi kusa, an kuma bashe Ɗan Mutum a hannuwan masu zunubi.
46 Mwimuke, Chigende. Lola, unu kandomela I iku afogee.”
Ku tashi, mu tafi! Ga mai bashe ni nan yana zuwa!”
47 Anu aliga achaika, Yuda oumwi wa bhaliya ekumi na bhabhili, nakinga. Liijo enene lyakingile amwi nage nilisokelela ku bhakulu bha bhagabhisi abhakulu na bhakaluka bhabhanu bhejile na amapanga na amalugujo.
Yayinda yana cikin magana, sai Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun nan, ya iso. Tare da shi kuwa ga taro mai yawa riƙe da takuba da sanduna, manyan firistoci da dattawan mutane ne suka turo su.
48 Nawe omunu oyo aliga eganilisishe okumulomela iniku Yesu aliga abhayanile echibalikisho, naika ati, “oyo nilamunyunya oyo niwe omwenene. Mumugwate.”
To, mai bashe shi ɗin, ya riga ya shirya alama da su, “Wanda na yi masa sumba, shi ne mutumin; ku kama shi.”
49 Ao nao naja ku Yesu naika ati, “Omulembe Mwiigisha!”Namunyunya.
Da zuwansa, sai ya miƙe zuwa wurin Yesu ya ce, “Gaisuwa, Rabbi!” Sa’an nan ya yi masa sumba.
50 Yesu namubhwila ati, “Musani likole linu lyakuleta.” Niwo nibhaja, nibhamulegela amabhoko Yesu, nibhamugwata.
Yesu ya amsa ya ce, “Aboki, yi abin da ya kawo ka.” Sa’an nan mutanen suka matso, suka kama Yesu suka riƙe shi.
51 Lola, omunu umwi unu aliga amwi na Yesu, agoloye okubhoko kwae nafulutula lipanga lyae. Namubhuma omugaya wo mugabhisi omukulu no kumutemako okutwi kwae.
Ganin haka, sai ɗaya daga cikin waɗanda suke tare da Yesu, ya zaro takobinsa ya kai wa bawan babban firist sara, ya fille masa kunne.
52 Mbe niwo Yesu namubhwila ati nusubye lipanga lyao ao walisosha, okubha bhona abho abhakolela lipanga bhalisingalisibhwa kwa lipanga.
Sai Yesu ya ce, masa, “Mai da takobinka kube, gama duk masu zare takobi, a takobi za su mutu.
53 Omutoga ati nitakutula okumubhilikila Lata wani wone nantumila abhasilikale bhakingile ekumi na bhabhili ga bhamalaika?
Kuna tsammani ba zan iya kira Ubana, nan take kuwa yă aiko mini fiye da rundunar mala’iku goma sha biyu ba?
54 Mbe nawe ka bhinu bhyandikilwe je bhikumile kutiki kutyo nikwo jiile jibhe kutyo?
Amma ta yaya za a cika Nassin da ya ce dole haka yă faru?”
55 Mu mwanya ogwo Yesu nalibhwila liijo, “Angu mwaja na mapanga na malugujo okungwata lwo musakusi? bhuli siku nenyajaga muyekalu niniigisya, na mutangwatile!
A wannan lokaci sai Yesu ya ce wa taron, “Ina jagoran wani tawaye ne, da kuka fito da takuba da kuma sanduna domin ku kama ni? Kowace rana ina zama a filin haikali ina koyarwa, ba ku kuwa kama ni ba.
56 Nawe gone ganu gakolekana koleleki amandiko ga bhalagi gakumile.” Niwo abheigisibhwa bhae nibhamusiga ni bhabhilima.
Amma wannan duka ya faru ne don a cika rubuce-rubucen annabawa.” Sa’an nan dukan almajiran suka yashe shi suka gudu.
57 Abho bhamugwatile Yesu bhamusilile ewa kayafa, omugabhisi omukulu olubhala lwa bhandiki na abhakaluka bhaliga bhekofyanyishe amwi.
Waɗanda suka kama Yesu kuwa suka kai shi wurin Kayifas, babban firist, inda malaman dokoki da dattawa suka taru.
58 Nawe Petro namulubhilila inyuma abhee kula. Okukinga mulugo lwo omugabhisi omukulu engie Munda nenyanja amwi na bhalisi alole chinu chilabhonekana.
Amma Bitrus ya bi daga nesa, har zuwa cikin filin gidan babban firist. Ya shiga, ya zauna tare da masu gadi, don yă ga ƙarshen abin.
59 Mbe abhakulu bha abhagabhisi na libhalaja lyona bhaliga nibhaeja obhu bhambasi bho olulimi ingulu ya Yesu kunsonga bhabhone okumwita.
Sai manyan firistoci da’yan majalisa duka suka yi ta neman shaidar ƙarya a kan Yesu, don su sami dama su kashe shi.
60 Nakabhee bhabhonekene abhabheelesha bhafu, nawe bhatabhwene njuno yone yone nawe bhejile bheya abhabheelesha bhabhili nibhaja imbele
Amma ba su sami ko ɗaya ba, ko da yake masu shaidar ƙarya da yawa sun firfito. A ƙarshe, biyu suka zo gaba,
61 nibhaika ati,”Omunu unu aikile ati, enitula okufumya liyekalu lya Nyamuanga no kulyumbaka Lindi kwa nsiku esatu.”'
suka furta cewa, “Wannan mutum ya ce, ‘Ina iya rushe haikalin Allah, in sāke gina shi cikin kwana uku.’”
62 Omugabhisi mukulu emeleguyu no kumubhusha ati, “utakutula kusubhya? bhanu abho abhakubhambalila chinuki ingulu yao?
Sa’an nan babban firist ya miƙe tsaye, ya ce wa Yesu, “Ba ka da wata amsa? Shaidar da mutanen nan suke yi a kanka fa?”
63 Nawe Yesu najibhila. Omugabhisi mukulu namubhwila ati, “lwa kutyo Nyamuanga alamile, nakulailila uchibhwile, alabha nawe Kristo, Omwana wa Nyamuanga.”
Amma Yesu ya yi shiru. Sai babban firist ya ce masa, “Na haɗa ka da Allah mai rai. Faɗa mana in kai ne Kiristi, Ɗan Allah.”
64 Yesu namusubhya ati, awe omwenene waika omusango ogwo. Nawe enikubhwila ati, okwambila wolyanu no kugendelela oumulola omwana wo munu enyanjile mukubhoko kwae okwebhulyo okwa managa na nejila mumele aga mulwile.”
Sai Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake yadda ka faɗa. Sai dai ina gaya muku duka, nan gaba, za ku ga Ɗan Mutum zaune a hannun dama na Mai Iko, yana kuma zuwa a kan gizagizan sama.”
65 Niwo omugabhisi omukulu natemula ebhifwalo bhyae naika ati, “Afuma! Angu echendaki lindi obhubheelesha nibhwaki? Lola, chimwi mwongwa nafuma.
Sa’an nan babban firist ya yage tufafinsa ya ce, “Ya yi saɓo! Don me muke bukatar ƙarin shaidu? Ga shi, yanzu kun dai ji saɓon.
66 Omwiganilisha kutiki? Nibhasubhya nibhaikana ati, “eile okufwa.”
Me kuka gani?” Suka amsa, suka ce, “Ya cancanci mutuwa.”
67 Mbe niwo nibhamufubhulila amachwanta mubhusu no kumubhuma jingumi, no kumuchapa amakofi kwa amabhoko gebhwe,
Sai suka tottofa masa miyau a fuskarsa, suka kuma bubbuge shi da hannuwansu. Waɗansu kuma suka mammare shi
68 Nibhaikana ati, “Nuchibhwile awe Kristo. Niga unu akuchapa?”
suka ce, “Yi mana annabci, Kiristi. Wa ya buge ka?”
69 Omwanya ogwo Petro aliga eyanjile anja mulugo, no mugaya we chigasi amulubhile naika ati, “Awe one wali uli amwi na Yesu wa Galilaya.”
To, Bitrus yana nan zaune a filin, sai wata yarinya baiwa, ta zo wurinsa. Ta ce, “Kai ma kana tare da Yesu mutumin Galili.”
70 Mbe nawe eganile imbele yabho bhone, naika ati nitakumenya chinu owaika.”
Amma ya yi mūsu a gabansu duka. Ya ce, “Ban san abin da kike magana ba.”
71 Ejile agenda anja yo lugo, omugaya oundi owe chigasi amulolele nabhabhwila bhanu bhaliga bhalio ao, “Omunu unu one aliga alio amwi na Yesu wa Najaleti.”
Sa’an nan ya fito zuwa hanyar shiga, inda wata yarinya kuma ta gan shi, ta ce wa mutanen da suke can, “Wannan mutum ma yana tare da Yesu Banazare.”
72 Negana lindi no kulaila ati, “Anye nitakumumenya omunu oyo.”
Ya sāke mūsu har da rantsuwa, yana cewa, “Ban ma san mutumin nan ba!”
73 Mwanya mutoto nigulabhao, bhanu bhaliga bhemeleguyu aei ao, bhamulubhile nibhaikana na Petro ati, “Nichimali kata awe one uli umwi webhwe, kwokubha nolwo inyaika yao eibhonekana.”
Bayan ɗan lokaci, sai na tsattsaye a wurin, suka hauro wurin Bitrus, suka ce, “Tabbatacce, kai ɗayansu ne, don harshen maganarka, ya tone ka.”
74 Mbe niwo namba okwifuma no kulaila ati, anye nitakumumenya omunu oyo,” Na aoela ing'oko nikokolima.
Sai ya fara la’antar kansa, yana ta rantsuwa yana ce musu, “Ban ma san mutumin nan ba!” Nan da take, sai zakara ya yi cara.
75 Petro ejukile emisango jinu abhwiliwe na Yesu ati, “eibha ing'oko ichali kukokolima oujokunyigana kwiya kasatu.”
Sai Bitrus ya tuna da maganar da Yesu ya yi cewa, “Kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sani na sau uku.” Sai ya fita waje, ya yi ta kuka.