< Marko 1 >

1 Bunu ni bwambilo bhwe misango jo bhwana eja Yesu Kristo, omwana wa Nyamuanga.
Farkon bishara game da Yesu Kiristi, Ɗan Allah.
2 Lwa kutyo jandikilwe no mulagi Isaya, “Lola, enimutuma omukosi wani imbele yao, oumwi unu kajo okuchuma-chuma injila yao.
An rubuta a cikin littafin annabi Ishaya cewa, “Zan aika da ɗan aikena yă sha gabanka, wanda zai shirya hanyarka,”
3 Obhulaka bhwo munu unu kabhilikila ibhala, “Ichumwe kisi injila ya Lata bhugenyi; Jigololwe kisi jinjila jae”.
“muryar mai kira a hamada tana cewa, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.’”
4 Yohana ejile, nabhatija ibhala no kusimula obhubhatijo bhwo kuta no kwiswalililwa ebhikayo.
Ta haka Yohanna ya zo, yana baftisma a yankin hamada, yana kuma wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
5 Echalo chona echa Yudea na abhanu bhona abha Yerusalemu bhagendele ewae. Bhaliga nibhabhatija nage mu mugela gwa Yordani, nibhegamba ebhibhibhi bhyebhwe.
Dukan ƙauyukan Yahudiya da dukan mutanen Urushalima suka fiffito zuwa wurinsa. Suna furta zunubansu, ya kuwa yi musu baftisma a Kogin Urdun.
6 Yohana aliga nafwala echifwalo bhwo bhufufi bhwa Ingamia na lifwata lyo lwai muchibhunu chae, na aliga nalya jinsige no bhuki bhwe mwila.
Yohanna ya sa tufafin gashin raƙumi, ya kuma yi ɗamara da fata. Abincinsa fāri ne da kuma zumar jeji.
7 Asimuye no kwaika, “Alio umwi unu kajokuja inyuma yani unu ankilile kula amanaga anye, nitana chibhalo nolwo okwinama emwalo no kusulumula jingoye je bhilato byae.
Wannan kuwa shi ne saƙonsa, “A bayana, wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban kuwa isa in sunkuya in kunce igiyar takalmansa ba.
8 Anye nabhabhatijishe mu maji, mbe nawe omwene kabhabhatija emwe mu Mwoyo Mwelu.”
Ina muku baftisma da ruwa, amma shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
9 Munaku ejo jabhonekene ati Yesu ejile okusoka Nazareti ya Galilaya, mbe nabhatijibhwa na Yohana mu mugela gwa Yordani.
A lokacin, Yesu ya zo daga Nazaret na Galili, Yohanna kuwa ya yi masa baftisma a Urdun.
10 Mu mwanya Yesu ejile enamuka okusoka mu maji, alolele olwile nilugabhanyika nabha abhwelu na Mwoyo namwikila namujako ali uti njibha.
Da Yesu yana fitowa daga ruwan, sai ya ga sama ya buɗe, Ruhu kuma yana saukowa a kansa kamar kurciya.
11 No bhulaka nibhusoka mu lwile, “Awe uli mwana wani omwendwa. Enikondelelwa muno nawe.”
Sai murya ta fito daga sama ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, da kai kuma nake fari ciki ƙwarai.”
12 Okumala ao nao Mwoyo namusinyilisha okuja ibhala.
Nan da nan, sai Ruhu ya kai shi cikin hamada,
13 Abheeyo ibhala naku makumi gana, nasakwa na Shetani. Aliga ali na jityanyi je mwila jindulu, na Bhamalaika nibhamufulubhendela.
ya kuma kasance a hamada kwana arba’in, Shaiɗan yana gwada shi. Yana tare da namomin jeji, mala’iku kuma suka yi masa hidima.
14 Oli ejile Yohana agwatibhwa, Yesu ejile Galilaya nalasha omusango gwo bhwana ogwa Nyamuanga,
Bayan da aka sa Yohanna a kurkuku, sai Yesu ya shigo cikin Galili, yana shelar bisharar Allah.
15 Naika,”Omwanya gwakumila, no bhukama bhwa Nyamuanga bhwelila ayei. Mute no kwikilisha mu musango gwo bhwana.”
Yana cewa, “Lokaci ya yi. Mulkin Allah ya yi kusa. Ku tuba, ku gaskata bishara!”
16 Anu aliga nalabha kunjejekela ya Galilaya, amulolele Simoni na Andrea owabho Simoni nibhatega emitego jebhwe mu nyanja, kwo kubha bhaliga bhategi.
Yayinda Yesu yake tafiya a gaɓar Tekun Galili, sai ya ga Siman da ɗan’uwansa Andarawus, suna jefa abin kamun kifi a cikin tafkin, domin su masunta ne.
17 Yesu abhabhwiliye, “Muje, mundubhe, ne enibhakola kubha bhategi bha bhanu.”
Yesu ya ce, “Ku zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masuntan mutane.”
18 Ao nao nibhajisiga emitego nibhamulibha.
Nan da nan, suka bar abin kamun kifinsu, suka bi shi.
19 Mu mwanya Yesu ejile alibhatao kula kutoto, amulolele Yakobho omwana wa Jebhedayo na Yohana omumula wabho; bhaliga mu bhwato nibhasobhola emitego.
Da ya yi gaba kaɗan, sai ya ga Yaƙub ɗan Zebedi, da ɗan’uwansa Yohanna a cikin jirgin ruwa, suna gyaran abin kamun kifinsu.
20 Okwiya nabhabhilikila na bhene nibhamusiga esemwene webhwe Jebhedayo mu bhwato na bhakosi bhanu bhaliga bhaliga bho kuliywa, nibhamulubha.
Ba da ɓata lokaci ba, ya kira su, sai suka bar mahaifinsu Zebedi a cikin jirgin ruwan, tare da’yan haya, suka kuwa bi shi.
21 Mbe bhejile bhakinga Kaperinaumu, mu lunaku olwa isabhato, Yesu engie mulikofyanyisho no kwiigisha.
Suka tafi Kafarnahum. Da ranar Asabbaci ta kewayo, sai Yesu ya shiga majami’a ya fara koyarwa.
22 Eliigisho lyae lyabhatang'ang'anyishe, lwa kutyo aliga nabheigisha lwo munu unu ali no bhutulo na atali lwa abhandiki.
Mutane suka yi mamakin koyarwarsa, domin ya koyar da su kamar wanda yake da iko, ba kamar malaman dokoki ba.
23 Mu mwanya ogwo ogwo aliga alio omunu mulikofyanyisho lyebhwe unu aliga no musambhwa mujabhi, aliga nakunga,
Nan take, sai wani mutum mai mugun ruhu a majami’arsu, ya ɗaga murya ya ce,
24 naika, “Chili na chinuki echokukola nawe, Yesu owa Nanjareti? Wijile okuchisimagisha? Enikumenya awe nawega. Awe nu Mulengelesi enyele owa Nyamuanga!”
“Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki nan na Allah!”
25 Yesu naligonya lisambwa elyo no kwaika, “Jibila na umusokemo!”
Yesu ya tsawata masa ya ce, “Yi shiru! Fita daga cikinsa!”
26 Mbe lisambwa lijabhi elyo nilimugwisha ansi mu mwanya ogwo namusokako nalila kwo bhulaka bhwa ingulu.
Sai mugun ruhun ya jijjiga mutumin da ƙarfi, ya fita daga jikinsa da ihu.
27 Mbe abhanu bhone nibhatang'ang'ala, kwibhyo nibhabhushanya bhuli umwi, “Chinu Niki? Eliigisho eyaya elyo bhutulo? Kalagilila amasambwa amajabhi ona agamuyana echibhalo!”
Dukan mutane suka yi mamaki, suna tambayar juna suna cewa, “Mene ne haka? Tabɗi! Yau ga sabuwar koyarwa kuma da iko! Yana ma ba wa mugayen ruhohi umarni, suna kuma yin masa biyayya.”
28 Emisango jo kulubhana no mwene nijitalala bhuli ebhala mu musi gwona ogwa Galilaya.
Labari game da shi ya bazu nan da nan ko’ina a dukan yankin Galili.
29 Na bhwangu wejile auluka mulikofyanyisho, bhengie mu nyumba ya Simoni na Andrea bhali Yakobho na Yohana.
Da suka bar majami’ar, sai suka tafi gidan su Siman da Andarawus, tare da Yaƙub da Yohanna.
30 Mbe woli nyabhuko Simoni aliga amamile ali mulwae wo muswija, bhwangu nibhamubhwila Yesu emisango jae.
Surukar Siman tana kwance da zazzaɓi, sai suka gaya wa Yesu game da ita.
31 Kwibhyo ejile, amugwatile no kubhoko, no kumwinamusha ingulu; Omuswija nigumusokako na namba okubhafulubhendela.
Sai ya je wajenta, ya kama hannunta, ya ɗaga ta. Zazzaɓin kuwa ya sāke ta, ta kuma yi musu hidima.
32 Kegolo eyo omwanya gwa lisubha lyalagae, bhamuletee ewae bhona bhanu bhaliga bhalwae, amwi na bhanu bhaliga bhaungilwe amasambwa.
A wannan yamma, bayan fāɗuwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan marasa lafiya, da masu aljanu.
33 Omusi gwona bhekofyanyishe amwi mu mulyango.
Duk garin ya taru a ƙofar gidan.
34 Abheulisishe bhwafu bhanu bhaliga bhalwae abha malwala ga bhuli mbaga no kusoshako amasambwa mafu, nawe atekilisishe amasambwa okwaika ku nsonga bhamumenyele.
Yesu kuwa ya warkar da marasa lafiya da yawa da suke da cututtuka iri-iri. Ya kuma fitar da aljanu da yawa, amma bai yarda aljanun suka yi magana ba, don sun san wane ne shi.
35 Emukile katondo mumachelelesha, chichali chisute; asokeleo no kuja ebhala lyo bhiibhise no kusabhwa eyo.
Da sassafe, tun da sauran duhu, Yesu ya tashi, ya bar gida, ya tafi wani wurin da ba kowa, a can ya yi addu’a.
36 Simoni na bhona bhanu bhaliga bhali amwi nage nibhamulubha.
Siman da abokansa suka fita nemansa.
37 Nibhamubhona mbe nibamubhwila, “Bhuli umwi kakuiga”.
Da suka same shi, sai suka ce, “Kowa yana nemanka!”
38 Abhabhwiliye, “Chigende ebhala lindi, anja mu misi jinu jiindile, koleleki eyo one nitule okusimula. Niyo insonga nijile anu.”
Yesu ya amsa ya ce, “Mu je wani wuri dabam, zuwa ƙauyukan da suke kusa, don in yi wa’azi a can ma. Wannan shi ne dalilin zuwana.”
39 Agendelee nalabha mu Galilaya Yona, nasimula mu mekofyanyisho gebhwe no kugonya amasambwa.
Sai ya tafi ko’ina a Galili, yana wa’azi a majami’unsu, yana kuma fitar da aljanu.
40 Omugege umwi namujako ku mwene. aliga namwilembeleja; Nafukama no kumubhwila, “Alabha owenda, outula okukola nibhe muanga.”
Wani mutum mai kuturta ya zo wurinsa, ya durƙusa ya roƙe shi ya ce, “In kana so, za ka iya tsabtacce ni.”
41 Nasindikwa ne chigogo, Yesu nagolola okubhoko kwae no kumukunyako,”Namubhwila, “Enenda. ubhe muanga.”
Cike da tausayi, sai Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka tsabtacce!”
42 Ao nao ebhigege nibhimusokako, na eulisibhwe nabha muanga.
Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi, ya kuma warke.
43 Yesu namukomelesha muno namubhwila agende bwangu,
Yesu ya sallame shi nan take, da gargaɗi mai ƙarfi cewa,
44 Amubhwilie, “komelesha ati utakutula kwaika musango ku wona wona, mbe nawe genda, uje okwiyelesha ku mugabhisi, na usoshe echogo kulwo kwela ku bhinu Musa alagilie, kuti bhubhambasi ku bhene.”
“Ka lura kada ka gaya wa kowa wannan. Amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayun da Musa ya umarta saboda tsarkakewarka, don yă zama shaida gare su.”
45 Mbe nawe agendele no kwamba okumubhwila Bhuli umwi no kulasha muno omusango nolwo Yesu atatulile lindi okwingila mu musi gwo abhwelu bhwelu. Kwibyo enyanjile enyelela na bhanu nibhamujako ku mwene okusoka bhuli ebhala.
A maimakon haka, sai ya fita, ya fara magana a sake, yana baza labarin. Saboda haka, Yesu bai ƙara iya shiga cikin gari a fili ba, sai dai ya kasance a wuraren da ba kowa. Duk da haka, mutane suka yi ta zuwa wurinsa daga ko’ina.

< Marko 1 >