< Marko 10 >
1 Yesu asokelao nagenda mumukoa gwobhuyaudi imbele yomugela gwayorodani, nalikumo lyabhanu nilimulubha bhuyaya. Nabheigisha bhuyaya, lwakutyo akolaga.
Yesu ya bar wannan wurin, ya tafi yankin Yahudiya, wajen hayin kogin Urdun. Sai jama'a suka je wurinsa. Ya ci gaba da koya masu, kamar yadda ya zama al'adarsa.
2 Amafarisayo bhejile okumusaka nibhamubhusha, “Nibhwakisi omulume okumusiga omugasi waye?”
Sai Farisawa su ka zo wurinsa, su ka ce, '' dai dai ne mutum ya saki matarsa?'' Wannan tambaya sun yi ta ne domin su gwada shi.
3 Yesu nabhabhwila, “Musa abhalagiliyeki?”
Ya amsa ya ce, menene Musa ya umarce ku?
4 Nibhaika, “Musa achibhwiliye okumwandikila echeti nomubhilimya.”
Suka ce, ''Musa ya yarda mutum ya rubuta takardar saki ga matarsa, ya sallameta ta fita.''
5 Kulwokubha emyoyo jemwe jikomee nicho ambhandikiye ichilagilo, Yesu nabhabhwila.
“Domin taurin zuciyarku ne ya rubuta maku wannan dokar,” Yesu ya ce masu.
6 Kubhwambilo bhwomogwa insi, 'Nyamuwanga amogele omulume no mugasi.'
Amman tun daga farkon halitta, 'Allah ya halicci namiji da ta mata.'
7 Kulwokubha Omulume kamusiga esemwene na nyilamwene nabha nomugasi waye,
Domin wannan dalilin ne mutum zai rabu mahaifinsa da mahaifiyarsa ya mannewa matarsa.
8 kubhone bhabhili abhabha chinu chimwi; kulwokubha bhatali bhabhili nawe mubhili gumwi.
Su biyu kuwa sun zama jiki daya, ba biyu ba,
9 Echo agwatenye Nyamuwanga, Omunu ataja ochitaganya.”
Saboda haka abinda Allah ya hada kada mutum ya raba.”
10 Bhaliga bhali munyanja, abhanafunzi bhaye nibhamubhusha bhuyaya ligambo elyo.
Lokacin da suke cikin gida, sai almajiransa suka sake tambayarsa akan wannan magana.
11 Nabhabhwila”Wonawona oyokamusiga amugasi waye natwala omugasi owundi, kakola echibhibhi kumwene.
Ya ce da su. Dukan wanda ya saki matarsa ya kuma auro wata matar yayi zina da ita kenan.
12 Omugasi akamusiga omulume natwalwa nomulume owundi, kakola echibhibhi.”
Haka nan duk matar da ta saki mijinta ta auri wani ta yi zina da shi kenan.”
13 Nibhamuletela abhana bhebhwe abhalela abhayane amabhando, tali abhanafunzi nibhabhaganya.
Mutane suka kawo masa 'ya'yansu kanana don ya taba su, sai almajiransa suka kwabe su.
14 Nawe Yesu ejile akamenya, atakondelesishwe nabhabhwila “Mubhasige abhana abhalela bhaje kwanye, kulwokubha abhanu lwabhanu obhukama bhwa Nyamuwanga nibhwebhwe.
Da Yesu ya gani, ya ji haushi, ya ce masu. Ku bar yara kanana su zo wurina, kada ku hana su domin mulkin Allah na irinsu ne.
15 Chimali enibhabhwila, Wonawona oyoatakulamila obhukama bhwa Nyamuwanga lwomwana omulela Chimali atakutula okwingila mubhukama bhwa Nyamuwanga.
Gaskiya na ke fada maku duk mutumin da bai karbi mulkin Allah kamar karamin yaro ba, babu shakka ba zai shiga mulkin Allah ba.
16 Niwo nabhayeka abhana mumabhoko gaye nabhayana amabhando nabhatelako amabhoko gaye ingulu yebhwe.
Sai ya rungume su ya sa masu albarka.
17 Ejile akamba olugendo lwaye munu umwi abhilimile nateja ebhijwi imbele yaye, namubhusha, “Mwiigisha wakisi, Nikole kutiki nibhulole obhukama bhwa kajanende?” (aiōnios )
Lokacin da ya fara tafiya, sai wani mutum ya rugo wurinsa, ya durkusa a gabansa. Ya tambaye shi, yace ya ''Malam managarci, me zan yi domin in sami rai na har abada?'' (aiōnios )
18 Yesu naika, “Kubhaki oumbilikila wakisi? Ataliwo oyo aliwakisi, Niwe Nyamuwanga wenyele.
Amma Yesu ya ce masa. Don me ka ke kira na managarci? Babu wani managarci sai dai Allah kadai.
19 Oumenya echilagilo: Utajakwita, utaja kusihana, utaja kwibha, utaika lulimi, utaja kujiga, bhayane echibhalo esomwana na nyokomwana.
Kasan dokokin. Kada ka yi kisan kai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar zur, kada ka yi zamba, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.”
20 Omunu uliya naika, “Mwiigisha, ganu gone nagamenyele nichali mulela.”
Sai mutumin ya ce masa Malam ai na kiyayye duk wadannan abubuwa tun ina yaro.
21 Yesu amuloleleye namwenda. Namubhwila “Oulebhya chinu chimwi. Owendibhwa okugusha bhinu bhyone ebhyo ulinabhyo nakubhayana abhataka, oubhona libhando mulwile. Niwouje undubhe.
Yesu ya dube shi duban kauna ya ce masa. Abu daya ka rasa. Shi ne ka je ka sayar da duk mallakarka ka ba mabukata, za ka sami wadata a sama. Sa'annan ka zo ka bi ni.
22 Nafwa omutima okubhwilwa amagambo ago, nagenda asulumbaye, kulwokubha aliga alimunibhi.
Da ya ji haka sai ransa ya baci, ya tafi yana bakin ciki, don shi mai arziki ne kwarai.
23 Yesu nalola wone nabhabhwila abhanafunzi bhaye, “Kukomee kumunibhi okwingila mubhukama bhwa Nyamuwanga!
Yesu ya dubi almajiransa ya ce. ''Yana da wuya masu arziki su shiga mulkin Allah!''
24 Abhanafunzi nibhalugushwa namagambo ago. Nawe Yesu nabhabhwila bhuyaya, “Abhana, nikukomee okwingila mubhukama bhwa Nyamuwanga!
Almajiransa suka yi mamakin maganarsa. Sai Yesu ce masu, ya ku ya'ya'na yana da wuya kamar me a shiga mulkin Allah.
25 Kwolobhele ingamiya okulabha mwiundu lya insiga, tali omunibhi okwingila mubhukama bhwa Nyamuwanga.”
Zai zama da sauki ga rakumi yabi ta kafar allura da mai arziki ya shiga mulkin Allah.
26 Bhalugulime muno nibhaikana, “Niga kakila”
Sai suka cika da mamaki sosai, su kace wa juna, ''to idan haka ne wanene zai iya tsira kenan?''
27 Yesu nabhalola naika, “Kumunu Kukomee, tali kunyamuwanga. kulwokubha Kunyamuwanga gone agatulikana.
Yesu ya dube su ya ce masu. Ga mutane a bu ne mai wuyar gaske, amma a wurin Allah komai yiwuwa ne.
28 Petro nambaokuloma nage, “Lola chasiga bhyone chakulubha.”
Bitrus ya ce masa, ''to gashi mu mun bar kome, mun bika''.
29 Yesu naika, “Chimali enibhabhwila emwe, ataliwo oyo asiga inyumba, nolo muyalawabho, nolo mutabhani wabho, nolo nyilamwene, nolo mwana, nolo esemwene, nolo insambu, nalubha anye naligambo lyani,
Yesu ya ce. Gaskiya na ke fada maku, babu wanda zai bar gidansa, da yan'uwansa maza da mata, da mahaifiya ko mahaifi, ko 'ya'ya ko gona, saboda da ni da kuma bishara,
30 Oyo alalema olamya egana muno kwaoli anu kuchalo: inyumba, mulawabho, muyalawabho, nyilamwene, abhana, isambu, kwonyaka, nainsi eyo eija nobhuwanga bhwa kajanende. (aiōn , aiōnios )
sa'annan ya rasa samun nikinsu dari a zamanin yanzu, na gidaje, da yan'uwa mata da maza' da iyaye mata da 'ya'ya da gonaki, game da tsanani, a duniya mai zuw kuma ya sami rai madawwami. (aiōn , aiōnios )
31 Tali abhanfu abhakubhwambilo bhalibha bhomalisha nabho bhalibha bhomalisha bhalibha bhokubhwambilo.
Da yawa wadanda suke na farko za su koma na karshe, na karshe kuma za su zama na farko.
32 Akatungu bhalimunjila, okuja Yerusalemu, Yesu aliga atangatileyo. Abhanafunzi nibhalugula, nabho bhaliga nibhabhasoka inyuma nibhobhaya. Niwo Yesu nabhasosha kumbali bhaliya ekumi nabhabhili namba okubhwilwa echochija okumubhona munaku jayeyi:
Suna tafiya Urushalima, Yesu kuwa na gabansu. Almajiransa sun yi mamaki, mutane da ke biye da su kuwa sun tsorata. Yesu kuwa ya sake kebe sha biyun nan, ya fara fada masu abin da zai same shi.
33 Lola, echigenda Yerusalemu, omwana womunu kakingibhwa kubhakuhani, abhakulu nabhandiki. abhamulamula afwe nabhalimusosha kubha nyamaanaga.
“Kun ga, za mu Urushalima za a bada Dan mutum ga manyan Firistoci da malan Attaura, za su kuma yi masa hukuncin kisa su kuma bada shi ga al'ummai.
34 Bhalimugaya, bhalimufubhulila amachwanta, bhalimubhuma najinsimbo, nabhamwita. Nawe kulunaku lwakasatu kasuluka.
Za su yi masa ba a, su tofa masa yau, su yi masa bulala, su kashe shi, bayan kwana uku kuwa zai tashi.”
35 Yakobho naYohana, abhana bha Zebedayo, bhejile kwaye nibhaika, “Mwiigisha, echikusabhwa uchikolele chonachona echochilakusabhwa.”
Yakubu da Yahaya, 'ya'yan Zabadi, suka zo wurin sa, suka ce, ''Malam muna so kayi mana duk abin da mu ka roke ka''
36 Nabhabhwila omwenda nibhakoleleki?
Ya ce masu. ''Me ku ke so in yi maku?''
37 Nibhaika chikilisishe chibhe bhone mubhukama bhwao, umwi mukubhoko kwolumosi aundi mukulyo.
Suka ce, ''ka yardar mana, a ranar daukakarka, mu zauna daya a damanka, daya kuma a hagunka.''
38 Tali Yesu nabhabhwila, “Mutakumenya echo omusabhwa.
Yesu ya ce masu. ''Ba ku san abinda ku ke roka ba. Kwa iya sha daga kokon da zan sha? Ko kuma za a yi maku baftismar da za a yi mani?''
39 nabhabhwila Omutula ochinywela echikompe echo nilachinywela nolo okubha mubhubhatijo obhwo nilabhatijibhwa, omubhutula.
Suka fada masa, ''Zamu iya.'' Yesu ya ce masu, '' kokon da zan sha, da shi zaku sha, baftismar da za ayi mani kuma da ita za a yi maku.''
40 Nawe oyokabha mukubhoko kwani kwokulyo aukwolumosi atalianye wososha, tali nibhaliya abho bhasolelwe.
Amma zama a damata, ko a haguna, ba na wa ba ne da zan bayar, ai na wadanda a ka shiryawa ne.”
41 Abhanafunzi abhandi ekumi bhejile bhakongwa ago, nibhamba okubha bhiililwa Yakobho naYohana.
Da sauran almajiran nan goma suka ji, suka fara jin haushin Yakubu da Yahaya.
42 Yesu nabhabhilikila kwaye naika, “Omumenya kutyo abhatangasha bhabhanu bhabhanyamaanga abhabhatangasha, nabhanu bhebhwe abhamenyekane abhabholesha obhutulo bhwebhwe.”
Yesu kuma ya kira su wurinsa ya ce masu, '' kun sani wadanda aka san su da mulkin al'ummai sukan nuna masu iko, hakimansu kuma sukan gasa masu iko.
43 Nawe kutalikisi okubha kutyo kwemwe.
Amma ba haka zai kasance a tsakaninku ba. Duk wanda ya ke son zama babba a cikinku, lalle ne ya zama baranku.
44 Wonawona oyo alabha mukulu agati yemwe abhatangashe, Wonawona oyo alibha wokwamba kwemwe kabha mukosi wabhona.
Duk wanda ya ke so ya shugabance ku lalle ne ya zama bawan kowa.
45 Kulwokubha omwana womunu atejile okukolelwa tali okutangasha, nokusosha isangama yaye kubhona.
Saboda haka ne Dan mutum ya zo ba domin a bauta masa ba, sai dai domin shi yayi bautar, ya kuma ba da ransa fansa saboda da mutane da yawa.”
46 Nibhaja Yeriko. Akasoka Yeriko nabhanafunzi bhaye nalikumo lyabhanu, Omwana waTimayo, Batimayo, Omuwofu omusabhilishi, eyanjile mumbali yainjila.
Sa'adda suka iso Yariko, yana fita daga Yariko kenan, shi da almajiransa, da wani babban taro, sai ga wani makaho mai bara, mai suna Bartimawas dan Timawas yana zaune a gefen hanya.
47 Ejile akongwa ni Yesu Munazareti, ambile okuyogana naika, “Yesu, Omwana wa Daudi, nsasila”
Da ya ji Yesu Banazare ne, ya fara daga murya yana cewa, ''Ya Yesu, Dan Dauda, kaji tausayina''
48 Bhanfu bhamuganyishe omuwofu, nibhamubhwila ajibhile. Nawe alilile elaka enene muno, “Mwana wa Daudi, Nsakila.”
Mutane da yawa suka kwabe shi, cewa yayi shiru. Sai ya kara daga murya kwarai da gaske, yana cewa, Ya Dan Dauda ka yi mani jinkai, ka ji tausayina!”
49 Yesu emeleguyu naika bhamulete. nibhamubhilikila omuofu uliya, nibhaika “Imuka Yesu kakubhilikila.”
Yesu ya tsaya ya ce, ku kirawo shi. Su kuwa suka kirawo makahon suka ce masa. ''Albishrinka, ta so! Yana kiranka.''
50 Nayesa ingubho ingubho yaye, nabhilima muno, naja kuyesu.
Makahon ya yar da mayafinsa, ya zaburo wurin Yesu.
51 Yesu namubhusha naika, “Owenda nikukoleleki?” Omulume uliya omuofu naika “Mwiigisha, enenda nilole.”
Yesu ya tambaye shi, ya ce, '' me ka ke so in yi maka?'' Makahon ya ce, ''Malam in sami gani.''
52 Yesu namubhwila, “Genda iimani yao yakwiulisha.” Awo awo amesoso gaye nigalola, namulubhilisha Yesu kunjila.
Yesu ya ce masa. ''Yi tafiyarka, bangaskiyarka ta warkar da kai.'' Nan take idanunsa suka bude, ya bi Yesu, suka tafi tare.