< Yoana 1 >

1 Kubwambilo gwaliga gulio Omusango, no Musango aliga amwi na Nyamuanga, Na Musango aligaali Nyamuanga.
Tun farar farawa akwai Kalma, Kalman kuwa yana nan tare da Allah, Kalman kuwa Allah ne.
2 Oyo, Musango, mubwambilo aliga amwi Na Nyamuanga.
Yana nan tare da Allah tun farar farawa.
3 Bhinu byona byakolelwe okutula kumwene atakabheye omwene chitalio nolwo chinu chimwi echo chakakolelwe.
Ta wurin Kalman ne aka halicci dukan abubuwa. In ba tare da shi ba, babu abin da aka yi wanda aka yi.
4 Bwikalo bhaye bhaliga bhuanga, no bhuanga bwaliga bwelu bwa bhanu bhona.
A cikinsa rai ya kasance, wannan rai kuwa shi ne hasken mutane.
5 Bwelu nibwatika muchisute, nolwo echisute chitalisimishe.
Hasken yana haskakawa cikin duhu, amma duhun bai rinjaye shi ba.
6 Aligaalio omunu oyo aliga atumwilwe okusoka Kunyamuanga unu lisina aliga Yohana.
Akwai wani mutumin da aka aiko daga Allah; mai suna Yohanna.
7 Ejile okubhambalila obwelu, koleleki bhatule okwikilisha okutula kumwene.
Ya zo a matsayin mai shaida domin yă ba da shaida game da wannan haske, don ta wurinsa dukan mutane su ba da gaskiya.
8 Yohana aliga atali bwelu, nawe ejile okubhambalila obwelu.
Shi kansa ba shi ne hasken ba; sai dai ya zo a matsayin shaida ne kaɗai ga hasken.
9 Obhwo bhwaliga bhuli bwelu bhwe echimali obhwo bhwaliga nibhuja muchalo obhwelu Obhwo nibhusosha obhwelu kubhuli munu.
Haske na gaskiya da yake ba da haske ga kowane mutum mai shigowa duniya.
10 Aligali musi, na isi yakolelwe okutula kumwene, na isi itamumenyele.
Yana a duniya, kuma ko da yake an yi duniya ta wurinsa ne, duniya ba tă gane shi ba.
11 Ejile kwe bhinu byaye, na bhamu bhatamulamiye.
Ya zo wurin abin da yake nasa, amma nasa ɗin ba su karɓe shi ba.
12 Nawe kwa bhafu bhanu bhamulamiye, bhekilisishe lisina lyaye, kwa bhanu abhayanile okubha bhana bha Nyamuanga,
Duk da haka dukan waɗanda suka karɓe shi, ga waɗanda suka gaskata a sunansa, ya ba su iko su zama’ya’yan Allah
13 Bhanu bhatebhuywe, atali kwa manyinga, okubha kwe lyenda lyo munu, nawe ku Nyamuanga wenyele.
’ya’yan da aka haifa ba bisa hanyar’yan adam, ko shawarar mutum ko nufin namiji ba, sai dai haifaffu bisa ga nufin Allah.
14 Newe musango nakolwa mubhili nekala kweswe, nichilola likusho lyaye, likusho lilabha lya munu wenyele oyo ejile okusoka ku Lata, ejuye echigongo ne chimali.
Kalman ya zama mutum, ya kuwa zauna a cikinmu. Muka ga ɗaukakarsa, ɗaukaka ta wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaici, wanda ya zo daga wurin Uba, cike da alheri da gaskiya.
15 Yohana nabhambalila omwene naikila ingulu ati,”Unu niwe naikile emisango jaye ninaika ati,”uliya kaja kulwani ni mukulu kukila anye, okubha abheyeo nichali anye.”
(Yohanna ya ba da shaida game da shi. Ya ɗaga murya yana cewa, “Wannan shi ne wanda na ce, ‘Mai zuwa bayana ya fi ni girma domin yana nan kafin ni.’”)
16 Kwo kubha okusoka mukukumila bwaye eswe chiyabhilwe kwe chigongo.
Daga yalwar alherinsa dukanmu muka sami albarka bisa albarka.
17 Okubha ebhilagilo bhiletelwe okutulila ku Musa. Echigongo nechimali byejile ku Yesu Kirsto.
Gama an ba da doka ta wurin Musa; alheri da gaskiya kuwa sun zo ne ta wurin Yesu Kiristi.
18 Atalio munu oyo amulolele Nyumuanga mwanya gwona. Omunu wenyele unu ni Nyamuanga, ali muchifubha cha Lata, amukolelede omwene bhamumenyega.
Ba wanda ya taɓa ganin Allah, sai dai Allah da yake Ɗaya da kuma Makaɗaici wanda yake a gefen Uba, shi ne ya bayyana shi.
19 Na bhunu nibhubhambasi bwa Yohana omwanya abhagabhisi na bhalawi bhamutumele kwaye na Bhayahudi nibhamubhusha ati, Awe niga?”
To, ga shaidar Yohanna sa’ad da Yahudawan Urushalima suka aiki firistoci da Lawiyawa su tambaye shi ko shi wane ne.
20 Nawe atetimatile atali, nabhasubya,”Anye atali Krisito.”
Bai yi mūsu ba, amma ya shaida a fili cewa, “Ba ni ne Kiristi ba.”
21 Kutyo nibhamubhusha ati,”kulwejo awe ni niga woli?” Awe ni Eliya? Naika ati,”Anye nitali.”nibhaika ati, Awe ni muligi? Nasubya,”Uli.”
Sai suka tambaye shi suka ce, “To, wane ne kai? Kai ne Iliya?” Ya ce, “A’a, ni ba shi ba ne.” “Kai ne Annabin nan?” Ya amsa ya ce, “A’a.”
22 Nibhamubwila ati,”Awe nawega, koleleki chibhayane lisubyo abhobhachitule”? Owibhambalilaatiki awe wenyele?”
A ƙarshe suka ce, “Wane ne kai? Ka ba mu amsa don mu mayar wa waɗanda suka aike mu. Me kake ce da kanka?”
23 Naika, “anye ni bhulaka bhaye unu ali ibhala:'Mugololele injila ya Lata bhugenyi Alabha omulagi Isaya kutyo aikile.”
Yohanna ya amsa da kalmomin annabi Ishaya, “Ni murya ne mai kira a hamada, ‘Ku miƙe hanya domin Ubangiji.’”
24 Bhaliga bhali bhanu bhatumilwe okusoka ku bhafalisayo. Nibhamubhusha ati ni bhaika,
To, waɗansu Farisiyawan da aka aika
25 “Kulwaki oubhatija labha awe atali Kristo amwi Eliya amwi mulagi?”
suka tambaye shi suka ce, “Don me kake yin baftisma in kai ba Kiristi ba ne, ba kuwa Iliya ba, ba kuma annabin nan ba?”
26 Yohana nabhasubya naika ati,”enibhatija kwa manji. Nolwo kutyo agati yemwe kemelegulu omunu oyo mutakumenya.
Yohanna ya amsa ya ce, “Ni dai ina baftisma da ruwa ne, amma a cikinku akwai wani tsaye da ba ku sani ba.
27 Unu niwe kaja kulwanye. Anye niteile kugesha olukobha lwa bhilato byaye.”
Shi ne mai zuwa bayana, wanda ko igiyar takalmansa ma ban isa in kunce ba.”
28 Emisago jinu jitagendeleye eyo Bethania, kungego ya Yorodani enu Yohana aliga nabhatija.
Wannan duk ya faru ne a Betani a ƙetaren Urdun, inda Yohanna yake yin baftisma.
29 Mwejo Yohana namulola Yesu naja kwaye naika ati,”Lola omwana wa inama wa Nyamuanga unu kagega ebhibhibhi bye chalo!
Kashegari Yohanna ya ga Yesu yana zuwa wajensa sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah mai ɗauke zunubin duniya!
30 Oyo niwe naikile emisango jaye ninaika ati,” oyo kaja inyuma yani ni mukulu kukila anye, okubha niwe atangatiye.'
Wannan shi ne wanda nake nufi sa’ad da na ce, ‘Mutum mai zuwa bayana ya fi ni girma, domin yana nan kafin ni.’
31 Nitamumenyele omwene, nawe yakolelwe kutyo koleleki abhulisibwe ku Israeli, ati nejile nimbatija kwa manji.”
Ko ni ma dā ban san shi ba, sai dai abin da ya sa na zo ina baftisma da ruwa shi ne domin a bayyana shi ga Isra’ila.”
32 Yohana nabhambalila,”nalola Omwoyo neka okusoka mulwile lwa injibha, ni mubhako ingulu yaye.
Sai Yohanna ya ba da wannan shaida, “Na ga Ruhu ya sauko kamar kurciya daga sama ya zauna a kansa.
33 Anye nitamumenyele nawe omwene oyo antumile nibhatije kwa manji nambwila ati, unu ulilola Omwoyo neka neyanja ingulu yaye, Oyo niwe kabhatija kwa Omwoyo Mwelu.'
Dā ban san shi ba, sai dai wanda ya aiko ni in yi baftisma da ruwa ya gaya mini cewa, ‘Mutumin da ka ga Ruhu ya sauko ya kuma zauna a kansa shi ne wanda zai yi baftisma da Ruhu Mai Tsarki.’
34 Nindola na nimbambalila ati onu ni Mwana wa Nyamuanga.”
Na gani na kuma shaida cewa wannan Ɗan Allah ne.”
35 Mwejo Yohana aliga emeleguyu amwi na bheigisibwa bhaye bhabhili,
Kashegari kuma Yohanna yana can tare da biyu daga cikin almajiransa.
36 Bhamulolele Yesu nalibhata na Yohana naika ati, Lola omwana wa inama wa Nyamuanga?”
Da ya ga Yesu yana wucewa, sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah!”
37 Abheigisibwa bhabhili nibhamugwa Yohana naika ati bhamulubhe Yesu.
Da almajiran nan biyu suka ji ya faɗi haka, sai suka bi Yesu.
38 Lindi Yesu nainduka na bhalola abheigisibwa bhaye nibhamulubha, nabhabwila ati, Omuyenjaki?” Ni bhamusubya ati,”Rabbi, (obhugajulo bwaye'mwiigisha,'wikaye aki?”
Da juyewa, sai Yesu ya ga suna bin sa, sai ya tambaye, su ya ce, “Me kuke nema?” Suka ce, “Rabbi” (wato, “Malam”), “ina kake da zama?”
39 Nabhabwila ati,”muje mulole.”Mbe nibhagenda nibhalola anu aliga ekaye; nibheyanja amwi nage lusiku olwo, Okubha yaliga uti saa ekumi kutya.
Ya amsa musu ya ce, “Ku zo, za ku kuma gani.” Saboda haka suka je suka ga inda yake da zama, suka kuma zauna a can tare da shi. Wajen sa’a ta goma ce kuwa.
40 Oumwi wa bhaliya bhabhili abhobhamunguwe Yohana naika no kumulubha Yesu aliga Andrea, owabho Simoni Petro.
Andarawus ɗan’uwan Siman Bitrus, yana ɗaya daga cikin biyun nan da suka bi Yesu bayan da suka ji maganar Yohanna a kan Yesu.
41 Namulola omula wabho Simoni na mubwila ati,”Chamulolele Masiya”(obhugajulo bwalyo ati Kristo).
Abu na fari da Andarawus ya yi shi ne ya sami ɗan’uwansa Siman ya gaya masa cewa, “Mun sami Almasihu” (wato, Kiristi).
42 Namuleta ku Yesu. Yesu namulolelela naika ati,”Awe ni Simoni omwana wa Yohana”ulibhilikilwa Kefa,”(obhugajulo bwalyo' Petro').
Ya kuma kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi ya ce, “Kai ne Siman ɗan Yohanna. Za a ce da kai Kefas” (in an fassara, Bitrus ke nan).
43 lusiku olwolwalubhiye omwanya Yesu nenda okugenda Galilaya, amubwene Filipo namubwila ati,”niundubhe anye.”
Kashegari Yesu ya yanke shawara yă tafi Galili. Da ya sami Filibus sai ya ce masa, “Bi ni.”
44 Filipo aligali wa Bethsaida, mu musi gwa Andrea na Petro.
Filibus, kamar Andarawus da Bitrus shi ma daga garin Betsaida ne.
45 Filipo namubhona Nathanaeli namubhila ati, Chamubhona uliya unu Musa andikile emisango jaye ne bhilagilo nabhalagi. Yesu omwana wa Yusufu, okusoka Nazareti.
Filibus ya sami Natanayel ya kuma gaya masa, “Mun sami wanda Musa ya rubuta game da shi a cikin Doka, kuma wanda annabawa suka rubuta a kansa, Yesu Banazare, ɗan Yusuf.”
46 Nathanaeli namubwila ati,”Mbe echinu chakisi echitula okusoka Nazareti?”Filipo namubwila ati, Ija olole.”
Natanayel ya ce, “A Nazaret! Wani abin kirki zai iya fito daga can?” Filibus ya ce, “Zo ka gani.”
47 Yesu namulola Nathanaeli naja kumwene naika ati,”Lola, Omwisraeli wechimali wechimali unu atali bhuligelige kwaye!”
Da Yesu ya ga Natanayel yana zuwa, sai ya yi magana game da shi cewa, “Ga mutumin Isra’ila na gaske wanda ba shi da ha’inci.”
48 Nathanaeli namubhwila ati,” Wamenyeyeaki anye?” yesu namusubya namubwila ati,”achali Filipo okubhilikila uli asi yo mutini, gwokulola.”
Natanayel ya yi tambaya ya ce, “A ina ka san ni?” Yesu ya amsa ya ce, “Na gan ka yayinda kake a gindin itacen ɓaure, kafin Filibus yă kira ka.”
49 Nathanaeli nasubya,”Rabi awe uli mwana wa Nyamuanga! Awe ni Mukama wa Israeli”!
Sai Natanayel ya ce, “Rabbi, kai Ɗan Allah ne. Kai ne Sarkin Isra’ila.”
50 Yeau nasubya namubwila ati, kwo kubha nakubwiliye' nakulolele asi yo mutini' mbe wekilisha? oulola ebhikolwa byafu okukila bhinu.”
Yesu ya ce, “Ka gaskata domin na ce maka na gan ka a gindin itacen ɓaure. Za ka ga abubuwan da suka fi haka.”
51 Yesu naika ati,”Nichimali chimali enibhabwila ati mulilola olwile lwigukile na mulibhalola bhamalaika nibhalinya na nibheka ingulu yo Mwana wa Nyamuanga.”
Sai ya ƙara da cewa, “Gaskiya nake gaya muku, za ku ga sama a buɗe, mala’ikun Allah kuma suna hawa suna kuma sauka a kan Ɗan Mutum.”

< Yoana 1 >