< Ebhikolwa bhya Jintumwa 3 >
1 Wori Petro na Yohana bhaliga mbagenda mwi hekalu omwanya gwo kusabhwa, saa mwenda.
Sa'adda Bitrus da Yahaya suna hanya zuwa haikali a lokacin addu'ar karfe uku.
2 Omunu kutya, omurema okusoka okwibhurwa, aliga nayekwa bhuli siku na aliga namamibhwa ku muryango gwa lihekalu ogwo ogubhilikirwa omukonde, korereki ature okusabha e bhiyanwa okusoka ku bhanu bhaliga mbagenda mwi hekalu.
Wani mutum, gurgu ne tun daga haihuwa, ana daukar sa kulluyomi zuwa kofar haikali da ake kira Kyakkyawa, domin bara gun mutanen da ke shiga haikalin.
3 Ejire abharora Petro na Yohana mbarebherera okwingira mwi hekalu, nasabhwa ebhiyanwa.
Da ya ga Bitrus da Yahaya suna shiga haikalin, sai ya roke su sadaka.
4 Petro, amukajisishe ameso, amwi na Yohana, aikile, “nuchirore eswe.”
Bitrus da Yahaya kuwa suka zuba masa ido, Bitrus ya ce, ''Ka dube mu.''
5 Omurema nabharora, netogera okubhona echinu kutya okusoka kubhene.
Gurgun nan kuwa ya dube su, yana tsammanin zai sami wani abu a wurin su.
6 Nawe Petro naika, “jiyera na jidhaabu anye ntanajo, nawe echo ninacho enisosha kwawe. Kwa lisina lya Yesu Kristo wa Nazareth, libhata.”
Amma Bitrus ya ce, “Azurfa da Zinariya ba ni da su, amma abin da nake da shi, zan baka. A cikin sunan Yesu Almasihu Banazare, Yi tafiya''
7 Petro namugega kwo kubhoko kwaye kwe bhuryo, namwimusha inguru: amaguru gaye ne bhikongochwa bhya mawa gaye mbijira amanaga.
Bitrus ya kama hannun damarsa, ya daga shi; nan da nan kafafunsa da kashin idon sawayensa suka samu karfi.
8 Nachuma inguru, omunu omurema nemereguru namba okulibhata; nengira mwi hekalu amwi na Petro na Yohana, nalibhata, nachuma, namukuya Nyamuanga.
Da gurgun ya yunkura, ya mike tsaye sai ya fara takawa; ya shiga haikali tare da Bitrus da Yahaya, yana takawa, yana tsalle, yana kuma girmama Allah.
9 Abhanu bhone bhamurorere nalibhata no kumukuya Nyamuanga.
Dukan mutane suka gan shi yana tafiya yana kuma yabon Allah.
10 Nibhamenya ati liga ali munu uliya oyo aliga neyanja nasabhwa ebhiyanwa ku muryango omukonde gwa lihekalu; nibhejurwa ne chiruguro no kutang'ang'ara kunjuno yecho chasokereye ku mwene.
Sun lura cewa, shine mutumin da ke zama yana bara a Kyakyawar kofar haikali; sai suka cika da mamaki domin abin da ya faru.
11 Kutyo aliga abhagwatirie Petro na Yohana, abhanu bhona amwi nibhabhilimira mu chisunya echo ehibhirikirwa cha Sulemani, nibharugura muno.
Yayin da yake rike da Bitrus da Yahaya, dukan jama'a suka matso wurinsu, a gefen dakalin Sulaimanu, suna ta mamaki kwarai.
12 Petro ejile alirora linu, omwene nabhasubhya abhanu, “Emwe abhanu bha Israeli, okubhaki omurugura? Okubhaki omurosha ameso gemwe kweswe, korere ati chamkora unu alibhate kwa managa geswe abhene?”
Da Bitrus ya ga haka ya amsa wa jama'ar, “Ya ku mutanen Isra'ila, don me ku ke mamaki?” Don me ku ka zura mana ido, kamar mu ne muka sa shi ya yi tafiya da ikon kanmu ko adalcin mu?
13 Nyamuanga wa Ibrahimu, no wa Isaka, no wa Yakobo, Nyamuanga wa bhalata bheswe, amukusishe omukosi waye Yesu. Unu niwe oyo emwe mwananire no kumurema imbele yo bhusu bhwa Pilato, nawe omwene aliga aramuye okumutatira obhweru.
Allah na Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, Allah na iyayenmu ya girmama bawansa Yesu. Shi kuka ki kun kuma bashe shi a gaban Bilatus da ya so ya sake shi.
14 Mwamuremere Mmweru no mulegeresi, na badala yo mwene nimwenda omwiti atatirwe.
Kuka ki Mai Tsarkin nan, Mai Adalcin, maimakon haka kuka ce a sakkar maku mai kisan kai.
15 Emwe mwamwitile Omukama wo bhujima, oyo Nyamuanga amwiruye okusoka mubhafuye eswe ni bhabhambasi bha linu.
Kun kashe mai ba da rai, wanda Allah ya tayar daga matattu, mu kuwa shaidu ne ga wannan al'amari.
16 Mbe oli, kwo kwikirisha mwi sina lyaye, omunu unu oyo omumurora no kumenya, akorerwe kubha na managa. Elikirisha eryo elirabha ku Yesu limuyanire omwene obhuanga bhunu bhugumile, imbele yemwe emwe bhona.
Yanzu, ta bangaskiya ga sunansa - wannan mutum da kuke gani kuma kun san shi - ta wurin wannan sunan ne ya sami karfi. Bangaskiya cikin Yesu ta ba shi cikakkiyar lafiya, a gabanku duka.
17 Mbe oli, Bhaili, enimenya ati mwakorere kutyo kwo bhumumu, nikwo kutyo bhakorere abhabhemberesi bhemwe.
Ya ku 'yan'uwa, na san kun yi haka ne cikin rashin sani, yadda shugabaninku suka yi.
18 Nawe amagambo ago Nyamuanga abhabhwiliye bhwangu kwe minwa ja bharagi bhona, ati unu Kristo kajonyaka, oli agamalire.
Amma duk abubuwan da Allah ya fada ta bakin dukan anabawansa, cewa Almasihunsa zai sha wahala, yanzu ya cika.
19 Mbe oli, mwigambe muinduke, korereki ati ebhiyeno bhyemwe bhisosibhweko chimwi, kunsonga gwije omwanya gwo kukondererwa okusokana no kubhao kwo Mukama;
Saboda haka, Ku tuba, ku juyo, domin a shafe zunubanku, domin lokacin sabuntuwa daga wurin Ubangiji ya zo;
20 na ati ature okumuragirira Kristo oyo asorerwe kwemwe, Yesu.
domin a aiko maku da Almasihu wanda aka kaddara wato, Yesu.
21 Omwene niwe oyo orwire lumuramire mpaka omwanya gwo kusubhya ebhinu bhyona, ebhyo Nyamuanga alomere kara kwe minwa ja bharagi bheru. (aiōn )
Shine wanda dole sama ta karbe shi har zuwa lokacin komo da dukan abubuwa, game da abubuwan da Allah ya fada tun da ta bakin annabawansa tsarkaka. (aiōn )
22 Ka chimwi Musa aikile, 'Omukama Nyamuanga kemusha omuragi lwanye okusoka mu bhaili bhemwe. Mumutegereshe bhuli chinu echo kabhabhwira emwe.
Musa hakika ya ce, 'Ubangiji Allah zai tayar maku da wani annabi kamar ni daga cikin, 'yan'uwanku. Za ku saurari dukan abin da zai fada maku.
23 Eisokerera ati bhuli munu oyo atakutegeresha ku muragi oyo ketibhwa chimwi asoke ku bhanu.'
Zai kasance kowanne mutum da bai saurari annabin nan ba za a kau da shi gabadaya daga cikin mutanensa.'
24 Yee, na bharagi bhona okusokerera Samweli na bhaliya bharubhile ku mwene, bharomere no kusimura jinsiku jinu.
I, dukan annabawa tun daga Sama'ila da wadanda suka zo bayansa, sun yi magana sun ambaci wadannan kwanaki.
25 Emwe muri bhana bha bharagi na bha liagano eryo Nyamuanga akorere amwi na bhakaruka, lwa kutyo aikire kwa Abrahamu, 'Mu mbegu yao jinganda jona eja kuchalo ejibharikiwa.'
Kune 'ya'yan annabawa da na alkawari wanda Allah ya yi da kakanninku, yadda ya ce wa Ibrahim, 'Daga zuriyarka dukan al'uman duniya za su sami albarka.'
26 Baada ya Nyamuanga okumukusha omukosi waye, amutumile kwemwe kwamba, korereki abhabariki emwe kwo kuinduka okusoka ku bhiyeno bhyemwe.
Bayan da Allah ya ta da bawansa, a gareku ne ya fara aiko shi, domin ya albarkace ku tawurin juyadda kowannenku daga muguntarsa.”