< 詩篇 73 >

1 アサフのうた 神はイスラエルにむかひ心のきよきものに對ひてまことに恵あり
Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
2 然はあれどわれはわが足つまづくばかりわが歩すべるばかりにてありき
Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
3 こはわれ惡きものの榮ゆるを見てその誇れる者をねたみしによる
Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
4 かれらは死るに苦しみなくそのちからは反てかたし
Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
5 かれらは人のごとく憂にをらず人のごとく患難にあふことなし
Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
6 このゆゑに倣慢は妝飾のごとくその頚をめぐり強暴はころものごとく彼等をおほへり
Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
7 かれら肥ふとりてその目とびいで心の欲にまさりて物をうるなり
Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
8 また嘲笑をなし惡をもて暴虐のことばをいだし高ぶりてものいふ
Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
9 その口を天におきその舌を地にあまねく往しむ
Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
10 このゆゑにかれの民はここにかへり水のみちたる杯をしぼりいだして
Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
11 いへらく神いかで知たまはんや至上者に知識あらんやと
Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
12 観よかれらは惡きものなるに常にやすらかにしてその富ましくははれり
Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
13 誠に我はいたづらに心をきよめ罪ををかさずして手をあらひたり
Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
14 そはわれ終日なやみにあひ朝ごとに責をうけしなり
Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
15 われもし斯ることを述んといひしならば我なんぢが子輩の代をあやまらせしならん
Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
16 われこれらの道理をしらんとして思ひめぐらししにわが眼いたく痛たり
Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
17 われ神の聖所にゆきてかれらの結局をふかく思へるまでは然りき
sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
18 誠になんぢはかれらを滑かなるところにおきかれらを滅亡におとしいれ給ふ
Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
19 かれらは瞬間にやぶれたるかな彼等は恐怖をもてことごとく滅びたり
Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
20 主よなんぢ目をさましてかれらが像をかろしめたまはんときは夢みし人の目さめたるがごとし
Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
21 わが心はうれへわが腎はさされたり
Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
22 われおろかにして知覺なし聖前にありて獣にひとしかりき
na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
23 されど我つねになんぢとともにあり汝わが右手をたもちたまへり
Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
24 なんぢその訓諭をもて我をみちびき後またわれをうけて榮光のうちに入たまはん
Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
25 汝のほかに我たれをか天にもたん地にはなんぢの他にわが慕ふものなし
Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
26 わが身とわが心とはおとろふされど神はわがこころの磐わがとこしへの嗣業なり
Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
27 観よなんぢに遠きものは滅びん汝をはなれて姦淫をおこなふ者はみななんぢ之をほろぼしたまひたり
Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
28 神にちかづき奉るは我によきことなり われは主ヱホバを避所としてそのもろもろの事跡をのべつたへん
Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.

< 詩篇 73 >