< 詩篇 50 >
1 アサフの歌 全能者なる神、主は詔して、日の出るところから日の入るところまであまねく地に住む者を召し集められる。
Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
2 神は麗しさのきわみであるシオンから光を放たれる。
Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
3 われらの神は来て、もだされない。み前には焼きつくす火があり、そのまわりには、はげしい暴風がある。
Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
4 神はその民をさばくために、上なる天および地に呼ばわれる、
Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
5 「いけにえをもってわたしと契約を結んだわが聖徒をわたしのもとに集めよ」と。
“Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
6 天は神の義をあらわす、神はみずから、さばきぬしだからである。 (セラ)
Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
7 「わが民よ、聞け、わたしは言う。イスラエルよ、わたしはあなたにむかってあかしをなす。わたしは神、あなたの神である。
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
8 わたしがあなたを責めるのは、あなたのいけにえのゆえではない。あなたの燔祭はいつもわたしの前にある。
Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
9 わたしはあなたの家から雄牛を取らない。またあなたのおりから雄やぎを取らない。
Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
10 林のすべての獣はわたしのもの、丘の上の千々の家畜もわたしのものである。
gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
11 わたしは空の鳥をことごとく知っている。野に動くすべてのものはわたしのものである。
Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
12 たといわたしは飢えても、あなたに告げない、世界とその中に満ちるものとはわたしのものだからである。
Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
13 わたしは雄牛の肉を食べ、雄やぎの血を飲むだろうか。
Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
14 感謝のいけにえを神にささげよ。あなたの誓いをいと高き者に果せ。
“Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
15 悩みの日にわたしを呼べ、わたしはあなたを助け、あなたはわたしをあがめるであろう」。
ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
16 しかし神は悪しき者に言われる、「あなたはなんの権利があってわたしの定めを述べ、わたしの契約を口にするのか。
Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
17 あなたは教を憎み、わたしの言葉を捨て去った。
Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
18 あなたは盗びとを見ればこれとむつみ、姦淫を行う者と交わる。
Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
19 あなたはその口を悪にわたし、あなたの舌はたばかりを仕組む。
Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
20 あなたは座してその兄弟をそしり、自分の母の子をののしる。
Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
21 あなたがこれらの事をしたのを、わたしが黙っていたので、あなたはわたしを全く自分とひとしい者と思った。しかしわたしはあなたを責め、あなたの目の前にその罪をならべる。
Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
22 神を忘れる者よ、このことを思え。さもないとわたしはあなたをかき裂く。そのときだれも助ける者はないであろう。
“Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
23 感謝のいけにえをささげる者はわたしをあがめる。自分のおこないを慎む者にはわたしは神の救を示す」。
Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”