< 詩篇 44 >

1 聖歌隊の指揮者によってうたわせたコラの子のマスキールの歌 神よ、いにしえ、われらの先祖たちの日に、あなたがなされたみわざを彼らがわれらに語ったのを耳で聞きました。
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
2 すなわちあなたはみ手をもって、もろもろの国民を追い払ってわれらの先祖たちを植え、またもろもろの民を悩まして、われらの先祖たちをふえ広がらせられました。
Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
3 彼らは自分のつるぎによって国を獲たのでなく、また自分の腕によって勝利を得たのでもありません。ただあなたの右の手、あなたの腕、あなたのみ顔の光によるのでした。あなたが彼らを恵まれたからです。
Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
4 あなたはわが王、わが神、ヤコブのために勝利を定められる方です。
Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
5 われらはあなたによって、あだを押し倒し、われらに立ちむかう者を、み名によって踏みにじるのです。
Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
6 わたしは自分の弓を頼まず、わたしのつるぎもまた、わたしを救うことができないからです。
Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
7 しかしあなたはわれらをあだから救い、われらを憎む者をはずかしめられました。
amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
8 われらは常に神によって誇り、とこしえにあなたのみ名に感謝するでしょう。 (セラ)
A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
9 ところがあなたはわれらを捨てて恥を負わせ、われらの軍勢と共に出て行かれませんでした。
Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
10 あなたがわれらをあだの前から退かせられたので、われらの敵は心のままにかすめ奪いました。
Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
11 あなたはわれらをほふられる羊のようにし、またもろもろの国民のなかに散らされました。
Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
12 あなたはわずかの金であなたの民を売り、彼らのために高い価を求められませんでした。
Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
13 あなたはわれらを隣り人にそしらせ、われらをめぐる者どもに侮らせ、あざけらせられました。
Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
14 またもろもろの国民のなかにわれらを笑い草とし、もろもろの民のなかに笑い者とされました。
Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
15 わがはずかしめはひねもすわたしの前にあり、恥はわたしの顔をおおいました。
Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
16 これはそしる者と、ののしる者の言葉により、敵と、恨みを報いる者のゆえによるのです。
saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
17 これらの事が皆われらに臨みましたが、われらはあなたを忘れず、あなたの契約にそむくことがありませんでした。
Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
18 われらの心はたじろがず、またわれらの歩みはあなたの道を離れませんでした。
Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
19 それでもあなたは山犬の住む所でわれらを砕き、暗やみをもってわれらをおおわれました。
Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
20 われらがもしわれらの神の名を忘れ、ほかの神に手を伸べたことがあったならば、
Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
21 神はこれを見あらわされないでしょうか。神は心の秘密をも知っておられるからです。
da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
22 ところがわれらはあなたのためにひねもす殺されて、ほふられる羊のようにみなされました。
Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
23 主よ、起きてください。なぜ眠っておられるのですか。目をさましてください。われらをとこしえに捨てないでください。
Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
24 なぜあなたはみ顔を隠されるのですか。なぜわれらの悩みと、しえたげをお忘れになるのですか。
Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
25 まことにわれらの魂はかがんで、ちりに伏し、われらのからだは土につきました。
An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
26 起きて、われらをお助けください。あなたのいつくしみのゆえに、われらをあがなってください。
Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.

< 詩篇 44 >