< 詩篇 108 >
1 ダビデの歌、さんび 神よ、わが心は定まりました。わが心は定まりました。わたしは歌い、かつほめたたえます。わが魂よ、さめよ。
Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
2 立琴よ、琴よ、さめよ。わたしはしののめを呼びさまします。
Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
3 主よ、わたしはもろもろの民の中であなたに感謝し、もろもろの国の中であなたをほめたたえます。
Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
4 あなたのいつくしみは大きく、天にまでおよびあなたのまことは雲にまで及ぶ。
Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
5 神よ、みずからを天よりも高くし、みさかえを全地の上にあげてください。
A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
6 あなたの愛される者が助けを得るために、右のみ手をもって救をほどこし、わたしに答えてください。
Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
7 神はその聖所で言われた、「わたしは大いなる喜びをもってシケムを分かち、スコテの谷を分かち与えよう。
Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
8 ギレアデはわたしのもの、マナセもわたしのものである。エフライムはわたしのかぶと、ユダはわたしのつえである。
Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
9 モアブはわたしの足だらい、エドムにはわたしのくつを投げる。ペリシテについては、かちどきをあげる」。
Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
10 だれがわたしを堅固な町に至らせるであろうか。だれがわたしをエドムに導くであろうか。
Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
11 神よ、あなたはわれらを捨てられたではありませんか。神よ、あなたはわれらの軍勢と共に出て行かれません。
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
12 われらに助けを与えて、あだにむかわせてください。人の助けはむなしいからです。
Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
13 われらは神によって勇ましく働きます。われらのあだを踏みにじる者は神だからです。
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.