< 使徒の働き 8 >

1 サウロは彼の死刑に同意していた。その日,エルサレムにあった集会に対して激しい迫害が起こった。使徒たちのほかは皆,ユダヤとサマリアの地方全域に散らされていった。
Bulus ya amince da mutuwarsa. A wannan rana tsanani mai zafi ya fara tasowa akan Iklisiya da take a Urushalima, sai masu bangaskiya duka suka bazu ko ina a cikin garuruwan Yahudiya da Samariya, sai manzannin kadai aka bari.
2 敬けんな人々はステファノを葬り,彼のために大いに嘆いた。
Amintattun mutane suka bizne Istifanus suka yi babban makoki game da shi.
3 一方,サウロは集会を荒らそうとして,すべての家に押し入り,男も女も引きずり出してはろうやに引き渡した。
Amma Shawulu ya yi wa Iklisiya mugunta kwarai, ya dinga shiga gida gida yana jawo mutane maza da mata, kuma yana kulle su cikin kurkuku.
4 それで,各地に散らされた人たちは,み言葉を宣教しながら巡回した。
Duk da haka masu bangaskiyar nan da suka warwatsu suka tafi suka dinga yada wa'azin maganar.
5 フィリポはサマリアの町に下って行き,人々にキリストを宣明した。
Filibus ya tafi can Samariya ya yi shelar Almasihu.
6 群衆は,フィリポが行なったしるしを見聞きすると,彼の語る事柄に心を合わせて聞き従った。
Da taron mutane suka ji kuma suka ga alamun da Filibus yake yi, sai suka mai da hankali dukansu domin su ji abinda yake fadi.
7 汚れた霊が取り付いていた多くの者から,それらが出て来たからである。それらは大声で叫びながら出て来た。体がまひした人や足の不自由な人が大勢いやされた。
Domin kazaman ruhohi sun fito daga cikin mutane da yawa da suka saurare shi suna kuka da kururuwa; nakasassun mutane dayawa da guragu suka warke.
8 この町には大きな喜びが起こった。
Kuma aka yi farin ciki mai girma a birnin.
9 ところで,そこにはある人がいたが,名をシモンといい,その町で以前から魔術を行なってサマリアの人々を驚かせ,自分を何か偉い者のように見せかけていた。
Amma akwai wani mutum a cikin birnin da ake kira Siman, wanda tun farko shi masafi ne da kuma dan dabo, yana yi wa mutanen Samariya abubuwan ban mamaki, yayin da yake kiran kansa wani mai muhimmanci.
10 最も小さな者から最も大きな者に至るまで,みんなが彼に聞き従い,「この人は神の偉大な力だ」と言っていた。
Dukan Samariyawa, manya da yara, suna sauraronsa, su kan ce, ''Wannan mutum shine ikon Allahn nan wanda ake kira mai girma.''
11 人々が彼に聞き従ったのは,彼が長い間,その魔術によって人々を驚かせてきたためであった。
Suna sauraron sa, domin ya dade yana yi masu abubuwan mamaki da tsafe-tsafensa.
12 ところが,人々は,神の王国とイエス・キリストの名についての良いたよりを宣教するフィリポを信じた時,男も女もバプテスマを受けた。
Amma da suka yi bangaskiya da wa'azin bisharar da Filibus yake yi game da mulkin Allah da sunan Yesu Almasihu, sai aka yi masu Baftisma dukansu maza da mata.
13 シモン自身もバプテスマを受けた。彼はバプテスマを受けると,いつもフィリポに伴っていた。しるしや大きな奇跡が起きるのを見て,驚いていた。
Har shima Siman da kansa ya ba da gaskiya. Bayan an yi masa Baftisma ya cigaba da bin Filibus, da ya ga ana nuna alamu da manyan ayyuka, sai ya yi mamaki.
14 さて,エルサレムにいた使徒たちは,サマリアが神の言葉を受け入れたと聞くと,ペトロとヨハネを彼らのもとに遣わした。
Da manzannin da ke Urushalima suka ji labarin Samariya ta karbi maganar Allah, sai suka aika masu Bitrus da Yahaya.
15 二人は下って行き,彼らが聖霊を受けるようにと彼らのために祈った。
Da suka iso, suka yi masu addu'a, domin su karbi Ruhu Mai Tsarki.
16 それがまだ彼らの中のだれにも下っていなかったからである。彼らは,ただキリスト・イエスの名においてバプテスマを受けていただけであった。
Domin har wannan lokaci, Ruhu Mai Tsarki bai sauko kan kowannensu ba; an dai yi masu baftisma ne kadai cikin sunan Ubangiji Yesu.
17 それで,二人が彼らの上に手を置くと,彼らは聖霊を受けた。
Sai Bitrus da Yahaya suka dora masu hannuwansu, sai suka karbi Ruhu Mai Tsarki.
18 その時,シモンは,使徒たちが手を置くことによって聖霊が与えられるのを見ると,二人にお金を差し出して
Sa'adda Siman yaga ana bayar da Ruhu Mai Tsarki ta wurin dorawar hannuwan manzanni, ya basu kudi.
19 言った,「わたしにもこの力を下さって,だれでもわたしが手を置く人が聖霊を受けられるようにしてください」。
Ya ce, “Ku bani wannan iko, ni ma, don duk wanda na dora wa hannu ya karbi Ruhu Mai Tsarki.''
20 しかしペトロは彼に言った,「あなたの銀はあなたと共に滅びてしまうがよい。あなたは神の贈り物をお金で得られると考えたからだ!
Amma Bitrus yace masa, ''Azurfarka ta lalace tare da kai, saboda kana tunanin za ka malaki baiwar Ubangiji da kudi.
21 あなたはこの事において受け分も分け前も持っていない。あなたの心が神の前にまっすぐでないからだ。
Baka da wani rabo a wannan al'amari, domin zuciyarka ba daidai take da Allah ba.
22 だから,この悪事を悔い改め,神に請い求めなさい。そうすれば,あなたの心の思いが許されることになるかも知れない。
Saboda haka ka tuba daga wannan muguntarka, ka kuma yi addu'a ga Ubangiji, domin mai yiwuwa ya gafarta maka game da manufar zuciyarka.
23 あなたが苦い胆汁と不法の束縛との中にいるのが,わたしには見えるからだ」。
Domin na gane kana cikin bacin rai da kuma cikin daurin zunubi.''
24 シモンは答えた,「皆さん,わたしのために主に祈ってください。あなた方の言われたことが何一つわたしに起こらないようにするためです」。
Siman ya amsa ya ce, ''Kayi addu'a ga Ubangiji domina, kada wani daga cikin abubuwan nan da ka fada ya faru da ni.''
25 このようにして,二人は証言して主の言葉を語ってから,エルサレムに引き返し,サマリア人の多くの村に福音を宣教した。
Sa'anda Bitrus da Yahaya suka bada shaida kuma suka fadi maganar Ubangiji, sun koma Urushalima; akan hanya, suka yi wa'azin bishara a kauyukan samariyawa da yawa.
26 一方,主のみ使いがフィリポに語りかけて,こう言った。「立って,南の方へ行き,エルサレムからガザに下る道に出なさい。そこは砂漠の道だ」。
Yanzu kuwa Mala'ikan Ubangiji ya yi wa Filibus magana cewa, ''Tashi ka tafi ta kudu da hanyar da ta yi kasa daga Urushalima zuwa Gaza'' (wannan hanyar yana cikin hamada.)
27 彼は立って出かけて行った。すると見よ,一人のエチオピア人がいた。エチオピア人の女王カンダケのもとで大きな権力を持つ宦官で,彼女の全財宝を管理していたが,礼拝のためにエルサレムに来ていた。
Ya kuwa tashi ya tafi. Sai ga wani mutum daga Habasha, baba ne mai babban matsayi a karkashin Kandakatu, sarauniyar Habasha. Shine yake mulkin dukan dukiyarta. Ya zo Urushalima domin ya yi ibada.
28 その帰りに,自分の戦車の中に座り,預言者イザヤを朗読していた。
Yana komawa zaune cikin karussarsa, kuma yana karanta Littafin annabi Ishaya.
29 霊がフィリポに言った,「近寄って,あの戦車と一緒に行きなさい」。
Ruhun ya ce wa Filibus, ''Ka je kusa da karussar nan.''
30 フィリポは走り寄り,彼が預言者イザヤを朗読しているのを聞いて,こう言った。「読んでいることが分かりますか」。
Sai Filibus ya gudu ya same shi, kuma ya ji shi yana karanta littafin annabi Ishaya, sai ya ce, ''Ka fahimci abin da kake karantawa?''
31 彼は言った,「だれかが説明してくれなければ,どうして分かるでしょうか」。そして,上がって来て自分と一緒に座ってくれるよう,フィリポに頼んだ。
Bahabashen ya ce. ''Yaya zan iya, idan ba wani ya bishe ni ba?'' Ya roki Filibus ya shigo cikin karussar ya zauna tare da shi.
32 ところで,彼が朗読していた聖書の箇所は,次のとおりであった。 「彼は羊のようにほふり場に引かれて行った。毛を刈る者の前で黙っている子羊のように,その口を開かない。
Wannan kuwa shine nassin da Bahabashen yake karantawa, ''An kai shi kamar tunkiya zuwa mayanka; shiru kuma, kamar dan rago a hannun masu sosayarsa, bai bude baki ba.
33 辱めを受け,その裁きは取り去られた。だれがその子孫のことを語るだろうか。その命は地から取り去られるからだ」。
Cikin kaskancinsa aka yi masa shari'a da rashin adalci: Wa zai bada tarihin tsararsa? Domin an dauke ransa daga duniya.''
34 宦官はフィリポに答えた,「この預言者はだれについて語っているのでしょうか。自分自身についてですか。それともだれかほかの人についてですか」。
Sai baban ya tambayi Filibus, ya ce, ''Na roke ka, gaya mani, game da wa annabin yake magana? Da kansa, ko kuwa wani mutum dabam?''
35 フィリポは口を開き,この聖句から始めて,彼にイエスのことを宣教した。
Filibus ya fara magana; akan littafin Ishaya, ya kuwa yi masa wa'azi akan Yesu.
36 彼らが進んで行くと,水のある所に来た。そこで宦官は言った,「ご覧ください,ここに水があります。わたしがバプテスマを受けるのに何の妨げがあるでしょうか」。
Yayin da suke tafiya akan hanya, sai suka iso bakin wani kogi; Baban ya ce, “Duba, ga ruwa anan; me zai hana ayi mani baftisma?”
Filibus ya ce,” Idan ka gaskanta da zuciya daya, ana iya yi maka baftisma.” Sai Bahabashen ya ce, “Na gaskata Yesu Almasihu shine Dan Allah.”
38 彼は戦車に止まるよう命じた。そして,フィリポと宦官は二人とも水の中に下りて行き,フィリポは彼にバプテスマを施した。
Sai Bahabashen ya umarta a tsai da karussar. Sai suka zo wurin ruwa dukan su biyu, Filibus da baban, Filibus kuwa yayi masa baftisma.
39 二人が水から上がると,主の霊がフィリポを連れ去ったので,宦官はもはや彼を見なかったが,喜びながら自分の道を進んで行った。
Yayin da suka fito daga cikin ruwan, Ruhun Ubangiji ya dauke Filibus; baban bai sake ganin shi ba, sai ya ci gaba da tafiyar sa yana murna.
40 一方,フィリポはアゾトスに現われた。すべての町々を通り抜けながら,福音を宣教し,ついにカエサレアに着いた。
Amma Filibus ya bayyana a Azotus. Ya ratsa wannan yankin yana wa'azin bishara a dukan garuruwan, har sa'anda ya iso Kaisariya.

< 使徒の働き 8 >