< 詩篇 69 >
1 神よねがはくは我をすくひたまへ 大水ながれきたりて我がたましひにまでおよべり
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
2 われ立止なきふかき泥の中にしづめり われ深水におちいるおほみづわが上をあふれすぐ
Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
3 われ歎息によりてつかれたり わが喉はかわき わが目はわが神をまちわびておとろへぬ
Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
4 故なくしてわれをにくむ者わがかしらの髮よりもおほく謂なくしてわが仇となり我をほろぼさんとするものの勢力つよし われ掠めざりしものをも償はせらる
Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
5 神よなんぢはわが愚なるをしりたまふ わがもろもろの罪はなんぢにかくれざるなり
Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
6 萬軍のヱホバ主よ ねがはくは汝をまちのぞむ者をわが故によりて辱かしめらるることなからしめたまへ イスラエルの神よねがはくはなんぢを求むる者をわが故によりて恥をおはしめらるることなからしめたまへ
Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
7 我はなんぢのために謗をおひ恥はわが面をおほひたればなり
Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
8 われわが兄弟には旅人のごとく わが母の子には外人のごとくなれり
Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
9 そはなんぢの家をおもふ熱心われをくらひ汝をそしるものの謗われにおよべり
gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
10 われ涙をながして食をたち わが霊魂をなげかすれば反てこれによりて謗をうく
Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
11 われ麁布をころもとなししにかれらが諺語となりぬ
sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
12 門にすわる者はわがうへをかたる われは酔狂たるものに謳ひはやされたり
Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
13 然はあれどヱホバよわれは惠のときに汝にいのる ねがはくは神よなんぢの憐憫のおほきによりて汝のすくひの眞實をもて我にこたへたまへ
Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
14 ねがはくは泥のなかより我をたすけいだして沈ざらしめたまへ 我をにくむものより深水よりたすけいだしたまへ
Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
15 大水われを淹ふことなく淵われをのむことなく坑その口をわがうへに閉ることなからしめたまへ
Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
16 ヱホバよねがはくは我にこたへたまへ なんぢの仁慈うるはしければなり なんぢの憐憫はおほしわれに歸りきたりたまへ
Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
17 面をなんぢの僕にかくしたまふなかれ われ迫りくるしめり ねがはくは速かに我にこたへたまへ
Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
18 わがたましひに近くよりて之をあがなひわが仇のゆゑに我をすくひたまへ
Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
19 汝はわがうくる謗とはぢと侮辱とをしりたまへり わが敵はみな汝のみまへにあり
Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
20 譭謗わが心をくだきぬれば我いたくわづらへり われ憐憫をあたふる者をまちたれど一人だになく慰むるものを俟たれど一人をもみざりき
Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
21 かれら苦草をわがくひものにあたへ わが渇けるときに醋をのませたり
Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
22 ねがはくは彼等のまへなる筵は網となり そのたのむ安逸はつひに羂となれ
Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
23 その目をくらくして見しめず その腰をつねにふるはしめたまへ
Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
24 願くはなんぢの忿恚をかれらのうへにそそぎ汝のいかりの猛烈をかれらに追及せたまへ
Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
25 かれらの屋をむなしくせよ その幕屋に人をすまはするなかれ
Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
26 かれらはなんぢが撃たまひたる者をせめ なんぢが傷けたまひたるものの痛をかたりふるればなり
Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
27 ねがはくはれらの不義に不義をくはへてなんぢの義にあづからせ給ふなかれ
Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
28 かれらを生命の册よりけして義きものとともに記さるることなからしめたまへ
Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
29 斯てわれはくるしみ且うれひあり 神よねがはくはなんぢの救われを高處におかんことを
Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
30 われ歌をもて神の名をほめたたへ 感謝をもて神をあがめまつらん
Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
31 此はをうしまたは角と蹄とある力つよき牡牛にまさりてヱホバよろこびたまはん
Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
32 謙遜者はこれを見てよろこべり 神をしたふ者よなんぢらの心はいくべし
Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
33 ヱホバは乏しきものの聲をきき その俘囚をかろしめたまはざればなり
Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
34 天地はヱホバをほめ蒼海とその中にうごくあらゆるものとはヱホバを讃まつるべし
Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
35 神はシオンをすくひユダのもろもろの邑を建たまふべければなり かれらは其處にすみ且これをおのが有とせん
gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
36 その僕のすゑも亦これを嗣その名をいつくしむ者その中にすまん
’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.