< 詩篇 37 >

1 惡をなすものの故をもて心をなやめ 不義をおこなふ者にむかひて嫉をおこすなかれ
Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
2 かれらはやがて草のごとくかりとられ靑菜のごとく打萎るべければなり
gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
3 ヱホバによりたのみて善をおこなへ この國にとどまり眞實をもて糧とせよ
Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
4 ヱホバによりて歓喜をなせ ヱホバはなんぢが心のねがひを汝にあたへたまはん
Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
5 なんぢの途をヱホバにゆだねよ 彼によりたのまば之をなしとげ
Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
6 光のごとくなんぢの義をあきらかにし午日のごとくなんぢの訟をあきらかにしたまはん
Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
7 なんぢヱホバのまへに口をつぐみ忍びてこれを俟望め おのが途をあゆみて榮るものの故をもて あしき謀略をとぐる人の故をもて心をなやむるなかれ
Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
8 怒をやめ忿恚をすてよ 心をなやむるなかれ これ惡をおこなふ方にうつらん
Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
9 そは惡をおこなふものは斷滅され ヱホバを俟望むものは國をつぐべければなり
Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
10 あしきものは久しからずしてうせん なんぢ細密にその處をおもひみるともあることなからん
A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
11 されど謙だるものは國をつぎ また平安のゆたかなるを樂まん
Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
12 惡きものは義きものにさからはんとて謀略をめぐらし之にむかひて切歯す
Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
13 主はあしきものを笑ひたまはん かれが日のきたるを見たまへばなり
amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
14 あしきものは劍をぬき弓をはりて苦しむものと貧しきものとをたふし行ひなほきものを殺さんとせり
Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
15 されどその劍はおのが胸をさしその弓はをらるべし
Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
16 義人のもてるもののすくなきは多くの惡きものの豊かなるにまされり
Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
17 そは惡きものの臂はをらるれどヱホバは義きものを扶持たまへばなり
gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
18 ヱホバは完全もののもろもろの日をしりたまふ かれらの嗣業はかぎりなく久しからん
Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
19 かれらは禍害にあふとき愧をおはず饑饉の日にもあくことを得ん
A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
20 あしき者ははろびヱホバのあたは牧場のさかえの枯るがごとくうせ烟のごとく消ゆかん
Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
21 あしき者はものかりて償はず 義きものは惠ありて施しあたふ
Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
22 神のことほぎたまふ人は國をつぎ 神ののろひたまふ人は斷滅さるべし
waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
23 人のあゆみはヱホバによりて定めらる そのゆく途をヱホバよろこびたまへり
In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
24 縦ひその人たふるることありとも全くうちふせらるることなし ヱホバかれが手をたすけ支へたまへばなり
ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
25 われむかし年わかくして今おいたれど 義者のすてられ或はその裔の糧こひありくを見しことなし
Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
26 ただしきものは終日めぐみありて貸あたふ その裔はさいはひなり
Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
27 惡をはなれて善をなせ 然ばなんぢの住居とこしへならん
Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
28 ヱホバは公平をこのみ その聖徒をすてたまはざればなり かれらは永遠にまもりたすけらるれど惡きもののすゑは斷滅さるべし
Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
29 ただしきものは國をつぎ その中にすまひてとこしへに及ばん
Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
30 ただしきものの口は智慧をかたり その舌は公平をのぶ
Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
31 かれが神の法はそのこころにあり そのあゆみは一歩だにすべることあらじ
Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
32 あしきものは義者をひそみうかがひて之をころさんとはかる
Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
33 ヱホバは義者をあしきものの手にのこしおきたまはず 審判のときに罰ひたまふことなし
amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
34 ヱホバを俟望みてその途をまもれ さらば汝をあげて國をつがせたまはん なんぢ惡者のたちほろぼさるる時にこれをみん
Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
35 我あしきものの猛くしてはびこれるを見るに生立たる地にさかえしげれる樹のごとし
Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
36 然れどもかれは逝ゆけり 視よたちまちに無なりぬ われ之をたづねしかど邁ことをえざりき
amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
37 完人に目をそそぎ直人をみよ 和平なる人には後あれど
Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
38 罪ををかすものらは共にほろぼされ惡きものの後はかならず斷るべければなり
Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
39 ただしきものの救はヱホバよりいづ ヱホバはかれらが辛苦のときの保砦なり
Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
40 ヱホバはかれらを助け かれらを解脱ちたまふ ヱホバはかれらを惡者よりときはなちて救ひたまふ かれらはヱホバをその避所とすればなり
Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.

< 詩篇 37 >